Connect with us

Labarai

Gudun tsinuwa: Wasu sun ƙi kai agaji ga motar Giyar da ta faɗi a Hisba

Published

on

Wasu daga cikin ganau kuma mazauna yankin na kan titin Panshekara, dab da Ofishin hukumar Hisba, da ke ƙaramar hukumar Kumbotso, sun ƙaurace wa bayar da gaji ga motar dakon Giyar da ta faɗi, domin gudun faɗawa cikin tsinuwar Allah, ga duk wanda ya taimaka ta kowace fuska cikin al’amari Giya.

Wakilin mu na ‘yan Zazu Ibrahim Abdullahi Soron Ɗinki ya na ɗauke da cikakken rahoton, ta cikin muryar da ke kasa.

Labarai

Ku tallafawa mabuƙata a cikin watan Ramadana don rage musu raɗaɗin rayuwa – Dr. Mujahedden

Published

on

Mataimakin Babban kwamandan Hisbah ta Jahar Kano Dakta Mujahideen Aminudden ya shawarci masu Hannu da shuni da su ƙara fitowa wajen tallawa masu ƙaramin ƙarfe musamman ma a wannan lokaci na azumin Ramadana, domin rage musu wani raɗaɗi da kuma samun gwaggwaɓar lada a wajen Ubangiji S.W.T.

Dakta Mujahedden Aminudden ya bayyana hakan ne yayin da ya ƙaddamar da rabon tallafin kayan Abinci ga iyayen Marayu da mabuƙata aƙalla su 2500, a yankin Nassarawa da ke nan Kano, domin rage musu wani radaɗin rayuwa musamman ma a watan nan na azumin Ramadana da ake ciki.

Da yake jawabi ga manema labarai Dakta Mujahideen, yayin rabon tallafin kayan abincin a ranar Asabar, ya ce sun bai wa mabuƙata da iyayen Marayu tallafin kayan abincin ne da suka haɗar da Shinkafa da Masara da Gero da kuma Burodi, domin rage musu wata damuwa ta yau da kullum don su samu wani sauƙi.

Dakta Aminudden ya kuma jinjinanwa gwamnatin jahar Kano, da babban kwamandan Hisbah a jihar Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, da ma ɗai-ɗai kun jama’a bisa gudunmawar da suke bayar wa wajen tallafawa mabuƙata.



Continue Reading

Labarai

Watan Azumi: Mun baza jam’ian mu na Operation Damisa Ƙisa Sabo don yaƙi da ɓata gari a Kano – Anty Snaching Phone

Published

on

Rundunar tsaron nan da ke yaƙi da faɗan Daba da ƙwacen waya da kuma daƙile Shaye-shayen kayan maye ta Anty Snaching Phone da ke nan Kano, ta buƙaci al’umma da su ƙara kula wajen rufe ƙofofin su yayin da za su tafi Sallar Dare, ta Tarawi da ta Tuhajjud da ke tafe a cikin wannan wata na Ramadana, domin gujewa faɗawa komar ɓata gari.

Kwamandan rundunar tsaron Inuwa Salisu Sharaɗa ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM Kano, ya kuma ce akwai buƙatar mutane su kaucewa yin sakaci wajen kula da muhallansu a cikin watan domin kaucewa haɗuwa da ɓata gari masu sace-sacen kayan mutane.

Inuwa Sharaɗa, ya kuma ƙara da cewa a ƙokarin su na daƙile harkokin ɓata garin da ke addabar mutane a sassan jihar Kano, tuni rundunar ta baza jam’ian ta domin ganin an kara wanzar da zaman lafiya a jihar.

“Jami’an mu suna kewayawa gurare daban-daban cikin dare da Rana, da ma kowanne lokaci, domin samar da tsaro ga al’umma, a cikin wannan wata na azumin Ramadana da wasu ke nauyin Bacci, “in ji shi”.

Inuwa Sharaɗa, wanda shi ne mai bai wa gwamnan jihar Kano shawara akan harkokin Tsaro, ya kuma buƙaci al’umma da su ci gaba da basu haɗin kan da ya dace, don ganin an samu nasara a yaƙin da suke yi da ɓata gari a sassan jihar.



Continue Reading

Labarai

Maulidin Inyass: Har yanzu babu wata matsalar tsaro da aka fuskanta a Kano – Anty Snaching Force

Published

on

Rundunar tsaro da ke yaƙi da faɗan Daba da ƙwacen Waya da kuma daƙile Shaye-shayen kayan maye ta Anty Snaching Force a Kano, ta ce kawo yammacin yau Asabar babu wata matsalar tsaro da aka samu a faɗin jihar, saɓanin wani rahoto da aka rinƙa yaɗawa a ranar Juma’a, cewar za’a iya fuskantar hakan.

Kwamandan rundunar, kuma mashawarci na musamman ga gwamnan Kano akan tsaro Inuwa Salisu Sharaɗa, ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da tashar Dala FM Kano, a yammacin yau Asabar 25-01-2025.

Wannan dai na zuwa ne a wani ɓangare na Maulidin Shehu Ibrahim Inyass da aka gudanar karo na 39, ranar Asabar a filin wasa na Sani Abacha Stadium da ke jihar Kano, wanda al’umma da dama daga sassan jahohihin Najeriya, da ma wasu ƙasashe suka halarta.

“Tun kafin a fara gudanar da maulidin Shehu Ibrahim Inyass, da lokacin gudanarwa har zuwa kammalawa, jami’an mu suka rinƙa zirga-zirga a cikin ƙwaryar birnin Kano, amma har zuwa yammacin yau ɗin nan ba mu samu wata matsala ta tsaro ba, “in ji Inuwa”.

A cewar sa, a zagayen da suka fara tun daga cikin daren jiya a ƙoƙarin su na daƙile matsalar tsaro yayin maulidin, sun kwana muna zirga-zirga a birnin Kano, tare da ziyartar irin su unguwannin Zango, da Hasiya Bayero, da Ƙofar Mata, da kuma gidan Murtala, da dai sauransu yankuna, baya ga zuba jami’an mu da muka yi a filin wasan na Sani Abacha Stadium.

Kwamandan rundunar tsaron ta Anty Snaching Force Inuwa Salisu, ya kuma buƙaci al’umma da su ci gaba da basu haɗin kai domin ganin an ƙara magance matsalolin tsaro a faɗin jihar Kano, da ma ƙasa baki ɗaya.

Daga cikin manyan baƙin da suka samu damar halartar taron Maulidin akwai Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf da mataimakinsa, da mai martaba Sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu, da Malamai, da ƴan Siyasa, da sauran al’umma.



Continue Reading

Trending