Connect with us

Labarai

Dalilan da suka sanya ShopRite ke son ficewa daga Najeriya

Published

on

Shararren kamfanin nan na Shoprite mallakin kasar Afirka ta kudu ya dakatar da ayyukansa a Najeriya

Kamfanin ya sanar da cewa ya fara gudanar da wani tsari da zai bashi damar dakatar da dukkanin ayyukansa a kasar.

Kamfanin Shoprite Holdings Limited ya ba da sanarwar a ranar Litinin a cikin rahoton hadar-hadarsa na shekara wanda ya kare a ranar 28 ga Yunin, 2020.

Kamfanin, wadanda ya sanar da samun karin kashi 6.4 cikin dari na ribar da ya samu duk da kalubalen da annobar Covid-19 ta haifar, ya ce ya dauki matakan dakatar da ayyukansa a Najeriya. “Sakamakon bukatar hakan daga masu zuba jari daban-daban, hakan ta sanya muka bullo da wannan matakin a Najeriya.”

“Hukumar gudanarwar kamfanin ta yanke shawarar fara sayar da dukkanin hannayen jari, ko kuma mafi yawa daga cikinsa, ga ‘yan kasuwa.

Duk da cewa kamfanin na iya samun karin wani kaso na musamman na hada-hadarsa, sai dai abun ba haka yake ba  a kasar Afirka ta Kudu.

A cewar rahoton, hadar-hadar tsagin kamfanin da ke wajen kasar Afirka ta Kudu amma ciki banda Najeriya sun samar da kashi 11.6 cikin dari na ribarsa, ko da yake an samu faduwar riba da kaso 1.4.

Shoprite ya danganta wannan koma baya da dokar kullen da aka samu a wasu kasashen Afirka da dama sakamakon barkewar annobar Coronavirus.

 

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending