Connect with us

Labarai

Unguwar Wailari sun yi gangamin jan kunne ga masu shaye-shaye

Published

on

Al’ummar unguwar Wailari da ke karamar hukumar Kumbotso sun gudanar da gangami domin wayar da kai da kuma jan kunne a kan matasan da ke ta’ammali da kayan maye da fataucin su a yankin.

Kwamandan kungiyar Bijilante na unguwar ta Wailari Abdullahi mai Karfi a zantawar sa da gidan rediyon Dala a ranar Talata ya ce, “Sakamakon abubuwan da ke faruwa a unguwar mu ta Wailari, nan ‘Yan Lemo, akwai wuri da a ke cewa ‘Yar Kwadi kowa yasan wuri ne na ‘yan daba, mutane su ka ce ba su yarda ba, mu ka kai takardar koke wajen jami’an tsaro, shi ne mu ka fito domin mu ja kunnen matasan… A jiya mata tara su ka shigo unguwar su na shaye-shaye, yaran nan ‘ya’yan mu ne da kannan mu, bama kyamar su, halin su ne bama so, burin mu su shiryu”. Inji Kwamanda

Kazalika, shugaban Kwamitin cigaban unguwar ta Wailari Umar Isah Bidda, shima ya bayyana dalilin yin gangamin na su ya na mai cewa, “Wannan shekara saboda karuwar yara masu shaye-shaye ya sanya an samu kisan kai, su n gayyato abokan su na wata unguwar lokacin biki, garin yin bikin ne kuma a ke kashe wasu”. A cewar shugaban Kwamiti

Malam Ibrahim Idris Dagacin Wailari ya ce, “Dama duk wani shugaba, hatta mai sarautar gargajiya burin sa al’umma su bayar da gudunmawa, su shigo domin dakile abubuwan da basu dace ba, domin wasu yaran baki ne ba ‘yan unguwa ba, dole sai an hada karfi da karfe domin kawo ci gaban unguwa”. Inji Dakaci

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending