Connect with us

Labarai

Karo na farko: An yi gwajin kwakwalwa ga masu niyyar aure a Kano

Published

on

A karo na farko an yi gwajin kwakwalwa ga masu niyyar yin aure a unguwar Danbare da ke jihar Kano domin dakile yawaitar rikicin ma’aurata wanda ke haddasa kashe-kashen juna.

Mai unguwar ta Danbare Saifullahi Abba Labaran ne ya bayyana hakan a zantawar sa da gidan rediyon Dala ranar Talata.

Ya ce, “Wannan doka mun dade da kafa ta, kuma wadannan bayin Allah da a ka yiwa gwajin mu na yi musu godiya, sakamakon hadin kai da su ka bamu. Wanda zai aure ta zuwa ya ke ya na a gini a unguwar, har a ka saba da shi kamar dan unguwa, ita kuma yarinyar a unguwar ta ke. Likitoci sun ce ya taba faduwa a mashin amma hakan ba wata matsala ba ce, ranar daurin aure za’a kawo takardar gwajin domin kowa yasan babu matsala a tare da su”.

Ya kuma ce, “Ko auro mace a ka yi za’a a shigo da ita unguwar sai mun tabbatar da an yi gwajin. Idan likitoci su ka nuna akwai matsala tsakanin mace ko namiji zamu sanar domin daukar matakin hana auren”. A cewar mai unguwa

Kazalika, shima matashin da zai yi auren ya ce, “Na yi farin ciki da wannan tsarin, an yi mana gwajin kwakwalwa, an kuma gano na taba faduwa a kan mashin, amma an ce ba wata matsala a auren mu, duk abubuwan da a ka zayyana na zama a unguwar na yarda da su. Ni ba asalin dan unguwar ba ne zuwa aikin gini na ke har mu ka saba da su”. Inji matashin

A nata bangaren, itama matashiyar da za’a aura ta ce, “Ni ba a same ni da matsala ba, kuma ‘yar asalin unguwar ce ni. Ina fatan za mu zauna ba matsala ni da shi, kuma zai zauna da ni babu kishiya insha Allahu”. A cewar matashiyar

Saifullahi Abba Labaran ya kuma ja hankalin hukumomi a sauran jihohi domin yin dokar gwajin kwakwalwa ga masu niyyar yin aure, wanda hakan zai kawo karshen kashe-kashe a tsakanin ma’aurata.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending