Connect with us

Labarai

A WATAN DISAMBAR BANA NE SABON JIRGIN SAMA MALLAKAR NAJERIYA ZAI FARA AIKI

Published

on

Ma’aikatar kula da harakokin sufurin jiragen sama a kasar nan, ta ce daga nan zuwa karshen wannan shekara ake fatan sabon kamfanin jirgin saman najeriya zai fara aiki.

Ministan ma’aikatar Hadi Sirika ne ya bayyana hakan, yayin da yake karbar takardar shedar amincewa da yarjejeniyar kasuwanci daga babban jami’in hukumar kula da mika ragamar tafiyar da kadarorin gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu (ICRC), injiniya Chidi Izuwah.

Ya ce, zuwa watan Disambar bana ake sa ran kamfanin jiragen saman na Najeriya zai fara aiki.

Sanata Hadi Sirika yayi bayanin cewa, kamfanin jirgin saman na hadin gwiwa ne da ‘yan kasuwa, yana mai cewa, matakin shine ma fi dacewa, kuma za’a dauki lokaci mai tsawo ana cin moriyarsa.

Ministan ya kuma musanta ikirarin da wasu ke yi cewa farfado da kamfanin jiragen saman na kasa zai durkusar da kamfanonin jiragen sama na ‘yan kasuwa dake aiki a kasar.

A hannu guda kuma wasu na ganin farfado da kamfanin jirgin sama na Najeriya zai taimaka wajen samun saukin tsadar farashin tikitin shiga jiragen sama na ‘yan kasuwa a Najeriya.

Ko da yake kamfanonin jiragen saman na cewa dole kujerar jirginsu ta yi tsada saboda yawan kudaden harajin da suke biyan gwamnati.

Baba Suda

Hukumar tattara kudaden shiga ta Kano ta rufe wasu bankuna

Published

on

Hukumar Tattara kudaden shiga ta jahar kano ta kulle bakin Eco da Zenith dake kan titin Murtala Muhammad. Sakamakon rashin biyan haraji.

Cikakken labarin na Zuwa….

Continue Reading

Baba Suda

Kisan Makurdi:- Gwamnatin Kano za ta tura wakilai

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano tayi Allah wadai da kisan mutane biyu Yan Jihar a garin Makurdi dake Jihar Benue.

Cikin sanarwar da Daraktan Gwamnan Kano kan harkokin yada labarai Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ruwaito Gwamnan na Mika sakon jaje ga alummar Jihar da iyalai da ‘yan uwan wadanda abin ya rutsa dasu, Barhma Suleman da Jamilu Ahmad.

 

Kazalika Gwamnan yayi alkawarin daukar Matakin da ya dace kan batun, tare da fadin gwamnatin Kano za ta tashi wakilai har Zuwa Jihar Benue domin tabbatar da daukar Matakin da ya dace.

 

 

Continue Reading

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Continue Reading

Trending