Connect with us

Labarai

IYAYE A GWALE SUN KOKA GAME DA RASHIN GURBIN KARATUN ‘YAYAN SU A ISLAMIYYA

Published

on

Iyaye a yankin kananan hukumomin Gwale da Kumbotso a nan Kano sun koka bisa rashin samun guraben da zasu sanya yayansu a Makarantar Tarbiyatul Aulad Chiranci Yamma, dake Chiranci a Karamar hukumar Kumbotso a nan Kano.

Wasu cikin Iyayen sun bayana cewar sun ziyarci harabar Makarantar tun da sanyin safiyar Asabar da ta gabata kamar yadda hukumar Makarantar ta shelanta don samarwa yayansu gurbi a Makarantar.

Sun kuma kara da cewar hukumar Makarantar ta kuma dakatar da sayar da takardar daukar daliban ne batare da mafi yawan su samu ba.

Sai dai Shugaban Makarantar ta Tarbiyatul Aulad Chiranci Yamma, Malam Mahadi Abdulmuminu Sulaiman, Cewa yayi suna bakin kokarinsu wajen daukar daliban amma karancin ajujuwa ne ya tilasta musu takaita daukar daliban.

Wakilin mu Abba Isah Muhammad, ya ruwaito cewa Iyaye da sauran mazauna yankin na fatan hukumar da gwamnati zasu rubanya kokarinsu wajen Inganta Iimi Musamman na Addinin Musulinci.

Baba Suda

Hukumar tattara kudaden shiga ta Kano ta rufe wasu bankuna

Published

on

Hukumar Tattara kudaden shiga ta jahar kano ta kulle bakin Eco da Zenith dake kan titin Murtala Muhammad. Sakamakon rashin biyan haraji.

Cikakken labarin na Zuwa….

Continue Reading

Baba Suda

Kisan Makurdi:- Gwamnatin Kano za ta tura wakilai

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano tayi Allah wadai da kisan mutane biyu Yan Jihar a garin Makurdi dake Jihar Benue.

Cikin sanarwar da Daraktan Gwamnan Kano kan harkokin yada labarai Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ruwaito Gwamnan na Mika sakon jaje ga alummar Jihar da iyalai da ‘yan uwan wadanda abin ya rutsa dasu, Barhma Suleman da Jamilu Ahmad.

 

Kazalika Gwamnan yayi alkawarin daukar Matakin da ya dace kan batun, tare da fadin gwamnatin Kano za ta tashi wakilai har Zuwa Jihar Benue domin tabbatar da daukar Matakin da ya dace.

 

 

Continue Reading

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Continue Reading

Trending