Connect with us

Labarai

AN KAMMALA TARON KUNGIYAR LAUYOYI MUSULMI NA YINI UKU DAYA GUDANA A NAN JIHAR KANO

Published

on

A jiya lahadi ne aka kammala taron kasa na yini uku da kungiyar lauyoyi musulmai wato MULAN a takaice ta shirya a nan Kano.

A yayin taron wadda ‘yayan kungiyar daga sasa daban daban na kasar nan sukahalarta, angabatar da kasidu daga masana a fannoni da damanarayuwa.

Taron na bana wadda shine karona 11, ya maida hankali ne akan batutuwan da suka shafi tsaron kasa, da ‘yancin bil’adama kana da kuma al’amuran ci gabaan rayuwar ‘yankasa.

Tsohon kwamishinan shari’a na jihar Kano Barrister Aliyu Umar SAN wanda shine shugaban kwamitin shirya taron ya yi karin haske dangane da makasudun kafa kungiyar lauyoyi musulmai a najeriya.

Shugaban kungiyar lauyoyi musulmai ta kasa reshen jihar Kano Barrister Ibrahim yace “ayyukan kungiyar baida kaita ga al’umar musulmi bakawai.”

Wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwato cewa, a karshen taron kungiyar na bana an fitar da takardar bayanin taron maikunshe da shawarwari ga gwamnati hukumomin tsaro, alkalai da lauyoyi da sauran masu ruwa da tsaki game da matakan inganta rayuwar ‘yan kasa musamman ta fuskar tabbatar da adalci a tsakanin ‘yankasa.

Baba Suda

Hukumar tattara kudaden shiga ta Kano ta rufe wasu bankuna

Published

on

Hukumar Tattara kudaden shiga ta jahar kano ta kulle bakin Eco da Zenith dake kan titin Murtala Muhammad. Sakamakon rashin biyan haraji.

Cikakken labarin na Zuwa….

Continue Reading

Baba Suda

Kisan Makurdi:- Gwamnatin Kano za ta tura wakilai

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano tayi Allah wadai da kisan mutane biyu Yan Jihar a garin Makurdi dake Jihar Benue.

Cikin sanarwar da Daraktan Gwamnan Kano kan harkokin yada labarai Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ruwaito Gwamnan na Mika sakon jaje ga alummar Jihar da iyalai da ‘yan uwan wadanda abin ya rutsa dasu, Barhma Suleman da Jamilu Ahmad.

 

Kazalika Gwamnan yayi alkawarin daukar Matakin da ya dace kan batun, tare da fadin gwamnatin Kano za ta tashi wakilai har Zuwa Jihar Benue domin tabbatar da daukar Matakin da ya dace.

 

 

Continue Reading

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Continue Reading

Trending