Connect with us

Labarai

AL’UMMAR UNGUWAR HOTORO SUN KOKA KAN YADDA HUKUMOMIN ILIMI SUKAYI WATSI DA TABARBAREWAR MAKARANTAR FIRAMAREN YANKIN

Published

on

Al’umar unguwar Hotoron Arewa a yankin karamar hukumar Nasarawa sun koka kan yadda hukumomin ilimi sukayi watsi da tabarbarewar yan aikin koyo da koyarwa a makarantar firamaren yankin.

Haka zalika, al’umomin sun bayyana damuwa kan yadda aikin gyaran titin unguwar ke tafiyar hawainiya tun bayan da gwamnati ta bada kwangilar gudanar da aikin.

A yayin ziyara ga dan majalisar dokokin Kano mai wakiltar karamar hukumar Nasarawa domin tunasar da hukumomin halin da suke ciki, shugaban tawagar al’ummomin Alhaji Muhammad Usman yace akwai bukatar mahukunta su kaimu su dauki domin ceto ilimin ‘yayan su daga durkushewa.

Da yake maida jawabi, wakilin Nasarawa a majalisar dokoki ta jihar Kano Alhaji Ibrahim Ahmad Gama yace “nan bada jimawa ba za’a fara aikin gudanar da garanbawul a makaranatar firamaren ta Hotoron arewa.”

Kansilan Hotoron Arewa, Alhaji Misbahu Auwal ya bayyana godiya a madadin al’umar yankinsa dangane da wannan mataki da gwamnati ta dauka akan batutuwan da suka koka akan su.

Wakilinmu Aminu Ahmad Abbas ya ruwaito cewa, ta kunshi dattawa da matasa da sauran masu ruwa da tsaki a yankin Hotoron arewa.

Baba Suda

Hukumar tattara kudaden shiga ta Kano ta rufe wasu bankuna

Published

on

Hukumar Tattara kudaden shiga ta jahar kano ta kulle bakin Eco da Zenith dake kan titin Murtala Muhammad. Sakamakon rashin biyan haraji.

Cikakken labarin na Zuwa….

Continue Reading

Baba Suda

Kisan Makurdi:- Gwamnatin Kano za ta tura wakilai

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano tayi Allah wadai da kisan mutane biyu Yan Jihar a garin Makurdi dake Jihar Benue.

Cikin sanarwar da Daraktan Gwamnan Kano kan harkokin yada labarai Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ruwaito Gwamnan na Mika sakon jaje ga alummar Jihar da iyalai da ‘yan uwan wadanda abin ya rutsa dasu, Barhma Suleman da Jamilu Ahmad.

 

Kazalika Gwamnan yayi alkawarin daukar Matakin da ya dace kan batun, tare da fadin gwamnatin Kano za ta tashi wakilai har Zuwa Jihar Benue domin tabbatar da daukar Matakin da ya dace.

 

 

Continue Reading

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Continue Reading

Trending