Labarai
KUNGIYAR KWADAGO TA KASA NLC TA RUFE OFISHIN KAMFANIN MTN A KANO

Kungiyar kwadago ta kasa reshen jihar Kano ta rufe ofishin kamfanin sadarwa na MTN saboda abin da kungiyar ta kira tauye hakkokin ma’aikatan kamfanin.
Da sanyin safiyar litinin din nan ce, kungiyar ta yi biyayya ga umarnin uwar kungiyar ta kasa wadda ke umartarr assan ta na fadin kasa su dauki wannan mataki domin tilastawa mahukuntan kamfanin na MTN suyi abinda ya kamata game da walwalar ma’aikatansa.
Kungiyar dai na zargin kamfaninna MTN da laifin hana ma’aikatansa kafawa ko kuma shiga kungiyoyin kwadago a kasar nan.
Shugaban kungiyar ta NLC na kasa reshen jihar Kano Comrade Kabiru Ado Minjibir yayi karin haske ga manema labarai game da wannan mataki.
Yace baya ga kamfanin MTN, kungiyar ta NLC zata dauki makaman cin wannan mataki a kan sauran kamfanonin sadarwa na kasar nan dake haramta wa ma’aikatan su shiga ko kuma kafa kungiyoyi da nufin gwagwarmayar kwato ‘yanci.
Babban Jami’i mai kula da ofishin kamfanin MTN na Kano Abdulhamid Hassan yace “tuni suka baiwa ma’aikatan su damar shiga kungiyoyi, yan amaicewa, kamfanin na kokari ainun wajen sauke hakkokin ma’aikata da ke rataye a wuyansa.”
Wakilinmu Auwal Rabiu Fanisau ya ruwaito cewa, a yayin gangamin rufe ofishin na MTN a nan Kano shugaban kungiyar ta NLC na tare da sauran jagororin kungiyar a nan jihar Kano.

Baba Suda
Hukumar tattara kudaden shiga ta Kano ta rufe wasu bankuna

Hukumar Tattara kudaden shiga ta jahar kano ta kulle bakin Eco da Zenith dake kan titin Murtala Muhammad. Sakamakon rashin biyan haraji.
Cikakken labarin na Zuwa….

Baba Suda
Kisan Makurdi:- Gwamnatin Kano za ta tura wakilai

Gwamnatin Jihar Kano tayi Allah wadai da kisan mutane biyu Yan Jihar a garin Makurdi dake Jihar Benue.
Cikin sanarwar da Daraktan Gwamnan Kano kan harkokin yada labarai Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ruwaito Gwamnan na Mika sakon jaje ga alummar Jihar da iyalai da ‘yan uwan wadanda abin ya rutsa dasu, Barhma Suleman da Jamilu Ahmad.
Kazalika Gwamnan yayi alkawarin daukar Matakin da ya dace kan batun, tare da fadin gwamnatin Kano za ta tashi wakilai har Zuwa Jihar Benue domin tabbatar da daukar Matakin da ya dace.

Baba Suda
NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.
Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.
A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.
Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

-
Nishadi6 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi6 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su