Connect with us

Labarai

An kubutar da wani mutum da a ka sakawa sasari tsawon shekaru 30

Published

on

Kungiyar kare hakkin dan adam mai suna Human Right Network, ta kubutar da wani mutum mai suna Murtala Muhammad mai shekaru 55, daga daurin Sasari da a ka yi masa a gida tsawon shekaru 30, a Kofar Fada da ke karamar hukumar Rogo a jihar Kano.

Shugaban kungiyar, Kwamared AA Haruna Ayagi ne ya bayyanawa Dala FM hakan jim kadan bayan kubutar da Murtala daga tsare shin da a ka yi, saboda lalurar tabin hankali da ya ke fama da ita.

Ya ce, “A safiyar nan ne labari ya zo mana abun da mu ka dade mu na bincikawa, domin mu gano gaskiyar lamarin, an kulle shi a gidan ne tun shekaru talatin da su ka gabata lokacin ya na da shekaru ashirin da biyar da haihuwa”.

Ya kuma ce, “Iyayen sa sun daure shi ne ta hanyar saka masa sasari a kafa ,sakamakon lalurar kwakwalwa, kuma tuni mu ka sanar da ‘yan sandan yankin karamar hukumar Rogo da taimakon su  a ka garzaya gidan a ka kubutar da shi daga cikin kangin”. A cewar Kwamared AA Haruna Ayagi

Shi ma mutumin Murtala Muhammad wanda ya magantu da kyar ya ce, “Na ji dadi da a ka kubutar da ni, domin ba na samun abinci yadda ya kamata ga kuma rashin fita da ba na yi”. Inji Murtala.

Wakilin mu Abubakar Sabo ya rawaito cewa, Kwamared AA Haruna Ayagi ya kuma ja hankalin iyayen da ke daure ‘ya’yan su da su guji yin hakan domin kungiyar su ba za ta bari a rinka cutar da su ba saboda matsalar tabin hankali.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending