Connect with us

Labarai

Wasu motoci 3 sun yi hadari a Kofar Kabuga

Published

on

Wani hadarin motoci guda a kofar Kabuga kan hanyar zuwa Jami’ar Yusuf Maitama Sule, ya janyo jikkatar al’umma.

Al’amarin ya faru a ranar Litinin, inda wata karamar mota kirar Toyota Corolla tare da wani kan DAF da baya dauke da bodi, suka doki juna har takai da ita Toyotar kifa saka makamakon dukan da kan DAF din.

Wasu da abun ya faru a kan idon su sun yi wa Wakilin mu Hassan Auwalu Muhammad karin haske.

“Na ga abun da ya faru, mot ace ta kwace ta daki wacce ta ke tafiya, inda wani mai motar yayi masa overtaking, burki ya kwace masa”. A cewar shaidar gani da ido

Shima mai karamar motar ta Corrolla, mai suna Malam Naziru Uba Muhammad, wanda da kyar a ka zaro shi daga cikin motar, sakamakon kifawar da ta yi, ya bayyana mana yadda abun ya faru.

“Ina tafiya a kan titi, sai mai babbar motar ya zo ya yi min dukan gefe, yazo zai yi min overtaking, ya na duka na motar ta kifa, daya motar tana gefe itama ya je ya dake ta.” Inji Malam Naziru

Nayi kokarin jin ta bakin direbobin DAF din, amman sunki yarda na dauki muryar su, to amman wani da yake cikin daya daga motocin DAF din mai suna Anas Ali ya ce, “Mu na cikin tafiya sai ji mu ka yi an dake mu, kuma ba kowa a gaban mu”. A cewar Anas Ali

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending