Connect with us

Labarai

Kotu na tuhumar matashi da bata sunan budurwa a Facebook

Published

on

Kotun majistret mai lamba 86 karkashin mai shari’a Faruk Ibrahim Umar ta sanya wani matshi a hannun beli.

Matashin mai suna Abubakar Muhammad a na zargin shi da laifin bata suna ta hanyar sanya hoton wata budurwa Aisha Ibrahim Babaji, ya hada ta da hotunan batsa ya na yadawa a dandalin sada zumunta na Facebook.

Yayin da a ka karanta tuhumar ya musanta zargin lauyan sa ya roki kotun da ta bayar da belin sa.

Mai shari’a Faruk Ibrahim Umar ya amince da rokon, sai dai ya ayyana cewar, sai an gabatar da mutum 2 masu kima kuma wadanda su ke da gida a karkashin hurumin kotun idan kuma ya tsere za su biya miliyan daya kowannen su.

A zantawar wakilin mu da lauyan mai kara Barista Husaini Ahmad Makari ya ce, “A na zargin Abubakar Muhammad ne da yada hoton batanci ga Aisha Babaji yayin da ya ke yanke fuskar ta yada hotunan tsiraici har ma da kawayen ta da su ka saka baki, bayan bincike a ka gano shi kuma a ka gurfanar da shi a gaban kotu”.

Itama Aishar ta bayyana yanda ta ji lokacin da hotunan ta suke yawo a Facebook tare da hotunan batsa.

Ta na mai cewa, “Mun hadu da shi ne a wajen aiki sai ya nuna ya na so na har ya ce zai turo nan bada dadewa ba, sai na ce ya yi hakuri sai nan gaba, shi ne ya dauki hotuna na ya na hadawa ya turawa kawaye na da ‘yan uwa na, ni yanzu ina so a bi min hakki na”. A cewar Aisha Babaji.

Lauyan da ya ke kare matashin, Barista Aliyu Umar Faruk ya bayyana matsayar su a kan batun inda ya ce, “Na farko dai tuhuma ce kamar yadda ‘yan sanda su ka saba yi, amma har yanzu a idon shari’a shi ba mai laifi ba ne, kamar yadda kundin tsarin mulkin kasa ya nuna, saboda haka kotu ce kawai za ta iya tabbatar da mai laifi ne ko ba mai laifi ba ne”.

Wakilin mu Yusuf Nadabo Isma’il ya rawaito cewa, Kotun ta sanya ranar 8 da 9 ga wata domin fara sauraron shaidu.

 

 

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending