Connect with us

Labarai

Kotu na tuhumar matashi da bata sunan budurwa a Facebook

Published

on

Kotun majistret mai lamba 86 karkashin mai shari’a Faruk Ibrahim Umar ta sanya wani matshi a hannun beli.

Matashin mai suna Abubakar Muhammad a na zargin shi da laifin bata suna ta hanyar sanya hoton wata budurwa Aisha Ibrahim Babaji, ya hada ta da hotunan batsa ya na yadawa a dandalin sada zumunta na Facebook.

Yayin da a ka karanta tuhumar ya musanta zargin lauyan sa ya roki kotun da ta bayar da belin sa.

Mai shari’a Faruk Ibrahim Umar ya amince da rokon, sai dai ya ayyana cewar, sai an gabatar da mutum 2 masu kima kuma wadanda su ke da gida a karkashin hurumin kotun idan kuma ya tsere za su biya miliyan daya kowannen su.

A zantawar wakilin mu da lauyan mai kara Barista Husaini Ahmad Makari ya ce, “A na zargin Abubakar Muhammad ne da yada hoton batanci ga Aisha Babaji yayin da ya ke yanke fuskar ta yada hotunan tsiraici har ma da kawayen ta da su ka saka baki, bayan bincike a ka gano shi kuma a ka gurfanar da shi a gaban kotu”.

Itama Aishar ta bayyana yanda ta ji lokacin da hotunan ta suke yawo a Facebook tare da hotunan batsa.

Ta na mai cewa, “Mun hadu da shi ne a wajen aiki sai ya nuna ya na so na har ya ce zai turo nan bada dadewa ba, sai na ce ya yi hakuri sai nan gaba, shi ne ya dauki hotuna na ya na hadawa ya turawa kawaye na da ‘yan uwa na, ni yanzu ina so a bi min hakki na”. A cewar Aisha Babaji.

Lauyan da ya ke kare matashin, Barista Aliyu Umar Faruk ya bayyana matsayar su a kan batun inda ya ce, “Na farko dai tuhuma ce kamar yadda ‘yan sanda su ka saba yi, amma har yanzu a idon shari’a shi ba mai laifi ba ne, kamar yadda kundin tsarin mulkin kasa ya nuna, saboda haka kotu ce kawai za ta iya tabbatar da mai laifi ne ko ba mai laifi ba ne”.

Wakilin mu Yusuf Nadabo Isma’il ya rawaito cewa, Kotun ta sanya ranar 8 da 9 ga wata domin fara sauraron shaidu.

 

 

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Trending