Connect with us

Labarai

Ƙarin ƙudin wuta zai iya sanyawa mu rage ma’aikata – Alhaji Sani Saleh

Published

on

Ƙungiyar masu masana’antu a unguwannin Bompai da Tokarawa a jihar Kano ta ce, ƙarin ƙudin wutar Lantarki da gwamnati ta yi kan iya haifar da rasa aiki ga wasu ma’aikatan su.

Shugaban ƙungiyar kuma mamba a ƙungiyar masu masana’antu ta ƙasa Alhaji Sani Saleh ne ya bayyana hakan a zantawar sa da Wakilin mu Bashir Sharfadi

Ya ce, “Wannan ƙarin da a ka yi, abu ne da yafi shafar mu kai tsaye duba ƙarin da mu ka samu cikin kuɗin wutar da mu ke biya, domin a yanzu ya kusa ninkawa zuwa gida biyu”.

Ya kuma ce, “Yanzu zabi biyu ne kaɗai ya rage mana, ƙarin farashi da kuma yiwuwar rage ma’aikatan mu”. Inji Alhaji Sani Saleh

A na sa ɓangaren Dr. Yusuf Ibrahim Ƙofar Mata, malami a jami’ar Yusuf Maitama Sule da ke jihar Kano, kuma masanin tattalin arziƙi ya ce, “Ko kaɗan babu hikima cikin wannan yin ƙari, mafita kawai shi ne gwamnati ta janye wannan ƙari ko kuma ta samar da hanyoyin rage raɗadi ga al’umma”. A cewar Dr. Yusuf Ibrahim Ƙofar Mata

Malam Usman Hassan Jakara daya daga cikin al’ummar jihar Kano ya ce, “Wannan ƙari ya zo mana ne a lokacin da ba mu shirya ba, akwai buƙatar gwamnati ta sake nazartar wannan mataki”. Inji Malam Usman Hassan Jakara

A farkon watan Satumban da mu ke ciki ne, kamfanonin samar da wutar lantarki a ƙasar nan, su ka fara amfani da sabon farashin wutar lantarki a faɗin ƙasar.

Kamfanonin dai sun ce, sun ɗauki wannan mataki ne bayan sauyin da hukumar kula da harkokin wutar lantarki ta kasa wato NERC ta yi.

Sabon tsarin dai ya karkasa masu amfani da wutar zuwa gida biyar, inda zai kasance kowa zai samu wuta daidai gwargwadon kuɗinsa, wato dai iya kuɗinka iya shagalinka.

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Trending