Connect with us

Labarai

Tun bayan ɓullar Corona jarin mu ya karye – Ƙananan ‘yan kasuwa

Published

on

Bayan ɓullar cutar Corona a Najeriya kawo wannan lokaci masu ƙananan sana’o na ci gaba da kokawa a kan ciniki da kuma durƙusar da tattalin arzikin su.

Sani Ibrahim mai laƙabin mai ‘yar sana’ar yara da ke sayar da soyayyar Doya a Garin Tiga da ke karamar hukumar Bebeji wanda ya kashe sama da shekaru goma sha shida ya na sana’ar.

Ya ce, “Annobar cutar Corona Virus ta yi mana matuƙar illa a harkar kasuwancin a yanzu wanda hakan yasa ba ni da jari sosai kamar yadda na ke da shi a baya ga kuma matsalar da a ke fama da ita”. Inji Sani Ibrahim

Haka zalika, Daya daga cikin masu gudanarda sana’ar sayar da kifi a kwanar Bagauda wato ‘yan Kifi.

Ya ce, “Yanzu ina rashin ciniki sosai, akwai bukatar gwamnati ta kawo mana ɗauki kasan cewar Cutar Corona ta yi mana illa”. Inji mai sana’ar sayar da kifi

Shima wani dattijo mai suna Alhaji Uba Tiga da ke gudanar da sana’ar kayan kanti wanda ya kwshe sama da shekaru arba’in ya na gudanarda da ita.

“Cinikin da mu ke yi a baya ko rabin sa ba ma yi a yanzu wanda hakan yasa jarina ya sami matsala sosai musamman a yanzu kasan cewar abaya jarina ya ɗara sama da naira dubu ɗari da takwas amma yanzu jarin nasa bai gaza dubu ɗari biyar ba domin duk ya yi amfani da ƙudin wajen ciyar da iyali a lokacin zaman kulle na Lockdown” A cewar Alhaji Uba Tiga

Wakilin mu Abdulkarim Muhammad Tukuntawa ya rawaito cewa, ‘Yan kasuwar a jihar Kano dai na cigaba da kira ga jama’a musamman gwamnati da a kawo musu ɗauki musamman waɗanda su ka gamu da iftila’in karyewar jarin su sakamakon ɓullar annobar cutar Corona a Kano da aka sha fama da ita wanda ta jefa rayuwar su da ta iyalansu cikin matsala a yanzu.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending