Connect with us

Labarai

Tun bayan ɓullar Corona jarin mu ya karye – Ƙananan ‘yan kasuwa

Published

on

Bayan ɓullar cutar Corona a Najeriya kawo wannan lokaci masu ƙananan sana’o na ci gaba da kokawa a kan ciniki da kuma durƙusar da tattalin arzikin su.

Sani Ibrahim mai laƙabin mai ‘yar sana’ar yara da ke sayar da soyayyar Doya a Garin Tiga da ke karamar hukumar Bebeji wanda ya kashe sama da shekaru goma sha shida ya na sana’ar.

Ya ce, “Annobar cutar Corona Virus ta yi mana matuƙar illa a harkar kasuwancin a yanzu wanda hakan yasa ba ni da jari sosai kamar yadda na ke da shi a baya ga kuma matsalar da a ke fama da ita”. Inji Sani Ibrahim

Haka zalika, Daya daga cikin masu gudanarda sana’ar sayar da kifi a kwanar Bagauda wato ‘yan Kifi.

Ya ce, “Yanzu ina rashin ciniki sosai, akwai bukatar gwamnati ta kawo mana ɗauki kasan cewar Cutar Corona ta yi mana illa”. Inji mai sana’ar sayar da kifi

Shima wani dattijo mai suna Alhaji Uba Tiga da ke gudanar da sana’ar kayan kanti wanda ya kwshe sama da shekaru arba’in ya na gudanarda da ita.

“Cinikin da mu ke yi a baya ko rabin sa ba ma yi a yanzu wanda hakan yasa jarina ya sami matsala sosai musamman a yanzu kasan cewar abaya jarina ya ɗara sama da naira dubu ɗari da takwas amma yanzu jarin nasa bai gaza dubu ɗari biyar ba domin duk ya yi amfani da ƙudin wajen ciyar da iyali a lokacin zaman kulle na Lockdown” A cewar Alhaji Uba Tiga

Wakilin mu Abdulkarim Muhammad Tukuntawa ya rawaito cewa, ‘Yan kasuwar a jihar Kano dai na cigaba da kira ga jama’a musamman gwamnati da a kawo musu ɗauki musamman waɗanda su ka gamu da iftila’in karyewar jarin su sakamakon ɓullar annobar cutar Corona a Kano da aka sha fama da ita wanda ta jefa rayuwar su da ta iyalansu cikin matsala a yanzu.

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Trending