Connect with us

Labarai

Mu na son gwamnatin Kano ta dakatar da ƙarin farashin dutse – Direbobin Tifa

Published

on

Ƙungiyar Direbobin Tifa ta kasa reshen jihar Kano ta bukaci gwamnatin Kano da ta dakatar da ƙarin ƙudin dutse da wasu kamfanonin ƙasar Sin da ke sarrafa duwatsu su ka yi musu da kusan kaso arba’in cikin ɗari ba tare da sun sanar da ƙungiyar ba.

Shugaban ƙungiyar Direbobin Tifa ta jihar Kano Kwamared Mamuni Ibrahim Takai ne ya bayyana hakan lokacin da yake zantawa da manema labarai kan batun ƙarin ƙudin da kamfanonin su ka yi wa masu siyan dutsen domin sanar da gwamnatin Kano.

Ya ce, Wannan ƙarin da kamfanonin su ka yi wa dutsen babu makawa zai haddasa tashin farashin dutsen a yanzu baya ga tsada da kwangila da za ta kara saboda ƙarin ƙudin, domin kuwa shima talaka gini zai gagareshi”.

Ya kuma ce, “Abun takaicin shi ne yadda al’ummar Kano su ke tarawa wadannan kamfanoni miliyoyin kuɗaɗen kuma duwatsun da su ke sarrafawa suna siyarwa da jama’a na ‘yan Kano ne kuma ’yan Kano ne su ke siya domin su yi amfani da shi”. A cewar Kwamared Mamuni Ibrahim Takai

Wakilin mu Abdulkarim Muhammad Tukuntawa ya rawaito cewar, shugaban kungiyar ya kuma yi ga gwamnati da ‘yan majalisar Kano harma da hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta jihar Kano da su takawa yunkurin kamfanonin birki domin mutane na cikin mawuyacin hali a yanzu.

 

 

 

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending