Connect with us

Wasanni

Cinikin ‘yan wasa: Liverpool ba za ta kashe kudi kamar na Chelsea ba – Klopp

Published

on

Mai horas da Liverpool Jurgen Klopp, ya ce kungiyar sa ta banbanta da sauran kungiyoyi wajen yadda sauran abokan hamayyar ta ke kashe makudan kudade wajen siyan ‘yan wasa.

Wannan batun na Kocin na zuwa ne yayin ganawar sa da wkiliyar BBC, dangane da yadda kungiyar Chelsea ke kashe makudan kudade wajen daukar ‘yan wasa a sabuwar kakar da za a fara.

Mai rike da kamun gasar Firimiya Liverpool ta dai kashe Fam miliyan 11.7 a bana wadda ta dauki dan wasa Tsimikas, a yayin da Chelsea ta kashe Fam miliyan 200 a hada-hadar kasuwancin ‘yan wasa a bana.

Mai horaswar ya ce“Abu ne mara tabbas yadda cutar Covid-19 ta haifar, zai zama mara amfani ga wasu, amma duk da mun kasance kungiya, ba za mu sauya lokaci guda ba, mu zama ko mu nuna dabi’ar irin yadda Chelsea ta yi a yanzu ba, mun banbanta da sauran kungiyoyin, saboda sau biyu mun je wasan karshe na cin kofin zakarun kungiyoyin nahiyar Turai, a zagaye na biyu ne mu ka lashe gasar, sannan mu ka lashe Firimiya duk da yadda mu ke a yanzu”. Inji Klopp.

Ko a shekarar bara, Liverpool ta kashe iya Fam miliyan 1.3 kawai, wanda ta dauki matashin dan wasan bayan kasar Holland, Sepp van den Berg daga kungiyar PEC Zwolle, inda ta daukimai tsaron raga Adrian da kuma Andy Lonergan a matsayin kyauta, sai kuma dan wasan gaban kungiyar, Red Bull Salzburg da ta dauka kuma dan kasar Japan, Takumi Minamino a wannan watan Janairu a kan kudi Fam miliyan 7.25.

Wasanni

Glesner ya zama sabon mai horas da Palace.

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace ta sanar da nadin Oliver Glesner a matsayin sabon mai horaswar ta.

Glesner wanda tsohon mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Eintracht Frankfurt ne mai shekaru 49 dan asalin kasar Austrian, ya maye gurbin tsohon mai horaswa Roy Hodson, wanda ake ganin ya gaza kai kungiyar ga tudun mun tsira.

A wasanni 16 da Crystal Palace ta buga a bayan nan ta yi rashin nasara a wasanni 10 duk karkashin jagorancin Roy Hodson wanda hakan yasa take mataki na 16 a teburin gasar firimiyar kasar Ingila.

Glesner dai ya rattaba kwantaragi da Palace har na tsawon shekaru biyu, zai kuma jagoranci kungiyar a wasan sa na farko da kungiyar kwallon kafa ta Burnley a ranar Asabar mai kamawa.

Continue Reading

Wasanni

Kasar Cote D’Ivoire ta yi nasara akan Najeriya 2-1, a gasar nahiyar Afrika ta Afcon 2023.

Published

on

Kasar Ivory Coast ta lashe gasar cin Kofin Nahiyar Afirka (AFCON) na 2023, bayan doke Najeriya da ci 2 da 1 a wasan karshe na gasar.

Rahotanni dai sun bayyana cewar mai masaukin bakin ta zama zakara ne, bayan ta warware kwallon da Najeriya ta jefa mata kafin tafiya hutun rabin lokaci a raga.

Yayin wasan dai dan wasan bayan Najeriya, Troost Ekoong ne ya fara jefa mata kwallo a minti na 38 a ragar Ivory Coast.

Sai dai kuma bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, Ivory Coast ta warware kwallon a minti na 62 ta hannun dan wasan tsakiyarta, Franck Kessie.

Yayin da aka kai munti na 81 Sebastian Haller ya kara wa mai masaukin baki kwallo ta biyu a raga, wanda hakan ya sanya ta zama zakarar AFCON ta 2023.

Yanzu haka dai ana shirye-shiryen bayar da kyauta ga kasar da ta yi nasara, da kuma wadanda aka shirya baiwa kyaututtukan, wanda kuma a wajen yanzu haka akwai mataimakin shugaban kasa Kasheem Shatima, da gwamnan jihar Katsina Umar Dikko Radda, da na jihar Nassarawa Abdullahi Sule, da kuma ministan Wasanni, da sauransu.

Idan ba a manta ba Najeriya ta doke Ivory Coast a wasan rukuni da suka fafata da ci daya ta hannun Troost Ekoong a bugun fanareti, kamar yadda jaridar Aminiya ta rawaito.

Continue Reading

Wasanni

Afcon2023: Ivory Coast za ta kara da Mali da yammacin yau Asabar

Published

on

A ci gaba da gasar cin kofin nahiyar Africa da ake fafatawa a kasar Cotdebua, a Asabar din nan ne tawagar masu masaukin baki Ivory Coast, za su fafata da kasar Mali, domin samun damar tsallakawa zagaye na daf da karshe a gasar.

Za dai a take wasan ne da misalin 6 na yamma yau, a filin wasa na Stade De Bouake.

Hakasalika suma kasar Cape Verd, za su kara da tawagar kasar Africa ta kudu a filin wasa na Stade Charles Konan Banny, da misalin karfe 9 na daren yau Asabar.

Ko a jiya ma dai wasan da aka buga tsakanin Najeriya da Ango, Super Eagle tayi nasara akan Ango da ci daya ba ko daya.

Continue Reading

Trending