Connect with us

Wasanni

Premier League: An kafa tarihi a farkon gasar ta bana

Published

on

Mai rike da kambun gasar Firimiyar kasar Ingila Liverpool, ta ci gaba da kafa tarihi a gasar na samun nasarar wasanni 60 ba tare da ta yi rashin nasara a gida ba.

Tun bayan da Chelsea ta yi wasanni 86 ba tare da an zura mata kwallo a gida ban tun a watan Oktobar shekarar 2008, sai kuma ita Liverpool wadda a watan Disambar shekarar 1980 ta taba kafa irin wannan tarihin na samun nasarar wasanni 63 ba tare da an zura mata kwallo a gida ba a gasar Firimiya.

Wannan da is hi ne gasar Firimiya ta biyu kenan da aka fara wasan farko a ka fara zura kwallaye 4 da 3 a wasan Leeds United da Liverpool, tun bayan da Manchester United ta fara zura kwallo 5 da 1 a ragar Fulham a karo na farkon fara wasan a watan Agusta na shekarar 2006, wanda a wasan zagayen farko ta zura kwallaye 4-1 a raga.

Kuma wannan shi ne karo na farko da a ka zurawa Liverpool kwallaye 3 a raga a wasan farko da Leeds United tun cikin shekarar 1982. Yanzu haka Liverpool ta samu nasarar wasanni 35 a gasar Firimiya wanda Mphammad Salah ya zura kwallaye 35 a raga cikin gasar, wanda a yanzu kuma ya yi ywa dan wasa Wayne Rooney fintinkau a gasar wanda ya zura kwallaye 34 a watan Satumba na shekarar 2008 da kuma watan Fabrairu na shekarar 2001.

Shi kuwa dan wasan bayan Liverpool, Virgil van Dijk ya zura kwallaye 10 a gasar da Liverpool, wanda ya fi kowane dan wasan baya zura kwallaye a gasar, tun lokacin da ya fara wasa a kungiyar a watan Janairun shekarar 2018, kuma duka kwallaye 9 da ya zura da kai ya zura su.

Dan wasan bayan Liverpool Van Dijk a cikin wasanni 154 da ya yi a Liverpool kwallaye 2 kawai ya jawo a ka zurawa Liverpool a raga.

Haka zalika Jack Harrison da Patrick Bamford da kuma Mateusz Klich sun kasance sababbin ‘yan wasa da su ka fara zura kwallaye a raga a farkon wasa a gasar Firimiya, tun bayan da dan wasan Leeds United Nick Barmby ya fara zura kwallo a farkon wasan sa a watan Agusta na shekarar 2002 a haduwar da su ka yi da Mancheseter City, wanda kuma ya kasance dan wasan da ya fara zura kwallo a waje tun bayan da Alan Smitth ya yi a watan Nuwamba na shekarar 1998 a Anfield gidan Liverpool.

Wasanni

Glesner ya zama sabon mai horas da Palace.

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace ta sanar da nadin Oliver Glesner a matsayin sabon mai horaswar ta.

Glesner wanda tsohon mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Eintracht Frankfurt ne mai shekaru 49 dan asalin kasar Austrian, ya maye gurbin tsohon mai horaswa Roy Hodson, wanda ake ganin ya gaza kai kungiyar ga tudun mun tsira.

A wasanni 16 da Crystal Palace ta buga a bayan nan ta yi rashin nasara a wasanni 10 duk karkashin jagorancin Roy Hodson wanda hakan yasa take mataki na 16 a teburin gasar firimiyar kasar Ingila.

Glesner dai ya rattaba kwantaragi da Palace har na tsawon shekaru biyu, zai kuma jagoranci kungiyar a wasan sa na farko da kungiyar kwallon kafa ta Burnley a ranar Asabar mai kamawa.

Continue Reading

Wasanni

Kasar Cote D’Ivoire ta yi nasara akan Najeriya 2-1, a gasar nahiyar Afrika ta Afcon 2023.

Published

on

Kasar Ivory Coast ta lashe gasar cin Kofin Nahiyar Afirka (AFCON) na 2023, bayan doke Najeriya da ci 2 da 1 a wasan karshe na gasar.

Rahotanni dai sun bayyana cewar mai masaukin bakin ta zama zakara ne, bayan ta warware kwallon da Najeriya ta jefa mata kafin tafiya hutun rabin lokaci a raga.

Yayin wasan dai dan wasan bayan Najeriya, Troost Ekoong ne ya fara jefa mata kwallo a minti na 38 a ragar Ivory Coast.

Sai dai kuma bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, Ivory Coast ta warware kwallon a minti na 62 ta hannun dan wasan tsakiyarta, Franck Kessie.

Yayin da aka kai munti na 81 Sebastian Haller ya kara wa mai masaukin baki kwallo ta biyu a raga, wanda hakan ya sanya ta zama zakarar AFCON ta 2023.

Yanzu haka dai ana shirye-shiryen bayar da kyauta ga kasar da ta yi nasara, da kuma wadanda aka shirya baiwa kyaututtukan, wanda kuma a wajen yanzu haka akwai mataimakin shugaban kasa Kasheem Shatima, da gwamnan jihar Katsina Umar Dikko Radda, da na jihar Nassarawa Abdullahi Sule, da kuma ministan Wasanni, da sauransu.

Idan ba a manta ba Najeriya ta doke Ivory Coast a wasan rukuni da suka fafata da ci daya ta hannun Troost Ekoong a bugun fanareti, kamar yadda jaridar Aminiya ta rawaito.

Continue Reading

Wasanni

Afcon2023: Ivory Coast za ta kara da Mali da yammacin yau Asabar

Published

on

A ci gaba da gasar cin kofin nahiyar Africa da ake fafatawa a kasar Cotdebua, a Asabar din nan ne tawagar masu masaukin baki Ivory Coast, za su fafata da kasar Mali, domin samun damar tsallakawa zagaye na daf da karshe a gasar.

Za dai a take wasan ne da misalin 6 na yamma yau, a filin wasa na Stade De Bouake.

Hakasalika suma kasar Cape Verd, za su kara da tawagar kasar Africa ta kudu a filin wasa na Stade Charles Konan Banny, da misalin karfe 9 na daren yau Asabar.

Ko a jiya ma dai wasan da aka buga tsakanin Najeriya da Ango, Super Eagle tayi nasara akan Ango da ci daya ba ko daya.

Continue Reading

Trending