Connect with us

Wasanni

Premier League: An kafa tarihi a farkon gasar ta bana

Published

on

Mai rike da kambun gasar Firimiyar kasar Ingila Liverpool, ta ci gaba da kafa tarihi a gasar na samun nasarar wasanni 60 ba tare da ta yi rashin nasara a gida ba.

Tun bayan da Chelsea ta yi wasanni 86 ba tare da an zura mata kwallo a gida ban tun a watan Oktobar shekarar 2008, sai kuma ita Liverpool wadda a watan Disambar shekarar 1980 ta taba kafa irin wannan tarihin na samun nasarar wasanni 63 ba tare da an zura mata kwallo a gida ba a gasar Firimiya.

Wannan da is hi ne gasar Firimiya ta biyu kenan da aka fara wasan farko a ka fara zura kwallaye 4 da 3 a wasan Leeds United da Liverpool, tun bayan da Manchester United ta fara zura kwallo 5 da 1 a ragar Fulham a karo na farkon fara wasan a watan Agusta na shekarar 2006, wanda a wasan zagayen farko ta zura kwallaye 4-1 a raga.

Kuma wannan shi ne karo na farko da a ka zurawa Liverpool kwallaye 3 a raga a wasan farko da Leeds United tun cikin shekarar 1982. Yanzu haka Liverpool ta samu nasarar wasanni 35 a gasar Firimiya wanda Mphammad Salah ya zura kwallaye 35 a raga cikin gasar, wanda a yanzu kuma ya yi ywa dan wasa Wayne Rooney fintinkau a gasar wanda ya zura kwallaye 34 a watan Satumba na shekarar 2008 da kuma watan Fabrairu na shekarar 2001.

Shi kuwa dan wasan bayan Liverpool, Virgil van Dijk ya zura kwallaye 10 a gasar da Liverpool, wanda ya fi kowane dan wasan baya zura kwallaye a gasar, tun lokacin da ya fara wasa a kungiyar a watan Janairun shekarar 2018, kuma duka kwallaye 9 da ya zura da kai ya zura su.

Dan wasan bayan Liverpool Van Dijk a cikin wasanni 154 da ya yi a Liverpool kwallaye 2 kawai ya jawo a ka zurawa Liverpool a raga.

Haka zalika Jack Harrison da Patrick Bamford da kuma Mateusz Klich sun kasance sababbin ‘yan wasa da su ka fara zura kwallaye a raga a farkon wasa a gasar Firimiya, tun bayan da dan wasan Leeds United Nick Barmby ya fara zura kwallo a farkon wasan sa a watan Agusta na shekarar 2002 a haduwar da su ka yi da Mancheseter City, wanda kuma ya kasance dan wasan da ya fara zura kwallo a waje tun bayan da Alan Smitth ya yi a watan Nuwamba na shekarar 1998 a Anfield gidan Liverpool.

Wasanni

Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta 2023/2024.

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta shekarar 2023/2024, bayan da suka samu nasara a kan Weder Bremen da ci 5-0.

Hakan ne kuma ya kawo ƙarshen shekaru 11 da Bayern Munich, da ta yi tana lashe gasar.

Wannan dai shi ne karo na farko da Bayer Leverkusen suka taɓa lashe gasar a tarihi, ida suka gaza ɗaukar kofin a shekarar 2002 a ranar ƙarshe ta gasar.

Har ila yau, a dai wannan shekarar ne su kayi rashin nasara hannun Shalke 04, a wasan ƙarshe na German Cup Da ci 4-2.

Haka kuma, Real Madrid suka doke su a wasan ƙarshe na zakarun nahiyar turai.

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar bata taɓa ɗaukar wata gasa ba a ƙarni na 21, sai bayan da Xavi Alonso ya karɓe su.

Continue Reading

Wasanni

Hukumar NPFL, ta amince da buƙatar Kano Pillars na ɗage wasan ta na mako na 28 da Enyimba

Published

on

Yanzu haka an samu dai-daito da hukumar NPFL, wanda ta amince da bukatar Kano Pillars na dage wasanta na mako na 28, da Enyimba zuwa ranar Alhamis, mai zuwa.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, ce ta wallafa hakan a shafin ta na Facebook da yammacin Litinin ɗin nan, ta ce ƴan wasan ta za su tashi a gobe Talata, da safe zuwa Aba domin fafata wasannin su.

Idan dai ba’a manta ba ƙungiyar ta wallafa kaɗan daga irin ƙalubalen da take fuskanta a harkokin gudanarwar ta.

Pillars, ta wallafa ƙalubalen ne kamar haka, “A yanzu haka zancan da muke muku Kano Pillars ta rasa kudin da za taje garin Aba, domin buga wasan hamayya na Nigeria Premier league wato Zobia Classic”.

Wasan dai shine wasa mafi ɗaukar hankali a league din Nigeria baki ɗaya, ku taya mu yadawa dan Allah.

Continue Reading

Wasanni

Glesner ya zama sabon mai horas da Palace.

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace ta sanar da nadin Oliver Glesner a matsayin sabon mai horaswar ta.

Glesner wanda tsohon mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Eintracht Frankfurt ne mai shekaru 49 dan asalin kasar Austrian, ya maye gurbin tsohon mai horaswa Roy Hodson, wanda ake ganin ya gaza kai kungiyar ga tudun mun tsira.

A wasanni 16 da Crystal Palace ta buga a bayan nan ta yi rashin nasara a wasanni 10 duk karkashin jagorancin Roy Hodson wanda hakan yasa take mataki na 16 a teburin gasar firimiyar kasar Ingila.

Glesner dai ya rattaba kwantaragi da Palace har na tsawon shekaru biyu, zai kuma jagoranci kungiyar a wasan sa na farko da kungiyar kwallon kafa ta Burnley a ranar Asabar mai kamawa.

Continue Reading

Trending