Connect with us

Wasanni

Bayern Munich: Ko kasan cewa a sansanin ‘yan gudun Hijira a ka haifi Davies?

Published

on

Dan wasan bayan gefen kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munich, Alphonso Davies wanda ya tallafawa Bayern Munich ta lashe kofi uku a kakar da ta gabata ciki harda Champoins League da Bundesliga tare da kuma Pokal Cup na kasar Jamus.

Dan wasan mai shekaru 19, wanda ya lashe kyautar Bundesliga Rookie award na kakar 2019-20, sakamakon rawar da ya taka.

Lokacin da ya daga Farantin gasar Bundesliga.

An dai haifi Davies ne a sansanin ‘yan gudun Hijira dake kasar Ghana, bayan da iyayen sa su ka gudu daga ainihin kasar su ta Liberia.

Davies da iyayen sa lokacin ya na da shekara biyar a duniya kuma shi ne daga farko daga kasa a kungiyar sa ta yara a kasar Canada.

Tun a wannan can lokaci iyayen dan wasan Davies su ka yi kaura zuwa kasar Canada a lokacin ya na dan shekara biyar da haihuwa, kuma a shekarar 2017 ne ya samu shaidar katin izini na zama a kasar Canada.

Davies ya na karami a daya gefen kuma ya daga kocin Champions League.

Davies ya kuma kasance dan wasa na farko a kasar Canada da ya taba zuwa wasan karshe a kasar a gasar cin kofin zakarun kungiyoyin nahiyar Turai, har ma ya samu damar lashe gasar a karo na farko a tarihin kasar da shi kan sa.

Yanzu haka dai tauraruwar dan wasan na haskakawa a Bayern Munich, tun bayan da ta dauke shi daga kungiyar Vancouver Whitecaps ta gasar MLS ta kasar Amurka a shekarar 2019.

Wasanni

Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta 2023/2024.

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta shekarar 2023/2024, bayan da suka samu nasara a kan Weder Bremen da ci 5-0.

Hakan ne kuma ya kawo ƙarshen shekaru 11 da Bayern Munich, da ta yi tana lashe gasar.

Wannan dai shi ne karo na farko da Bayer Leverkusen suka taɓa lashe gasar a tarihi, ida suka gaza ɗaukar kofin a shekarar 2002 a ranar ƙarshe ta gasar.

Har ila yau, a dai wannan shekarar ne su kayi rashin nasara hannun Shalke 04, a wasan ƙarshe na German Cup Da ci 4-2.

Haka kuma, Real Madrid suka doke su a wasan ƙarshe na zakarun nahiyar turai.

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar bata taɓa ɗaukar wata gasa ba a ƙarni na 21, sai bayan da Xavi Alonso ya karɓe su.

Continue Reading

Wasanni

Hukumar NPFL, ta amince da buƙatar Kano Pillars na ɗage wasan ta na mako na 28 da Enyimba

Published

on

Yanzu haka an samu dai-daito da hukumar NPFL, wanda ta amince da bukatar Kano Pillars na dage wasanta na mako na 28, da Enyimba zuwa ranar Alhamis, mai zuwa.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, ce ta wallafa hakan a shafin ta na Facebook da yammacin Litinin ɗin nan, ta ce ƴan wasan ta za su tashi a gobe Talata, da safe zuwa Aba domin fafata wasannin su.

Idan dai ba’a manta ba ƙungiyar ta wallafa kaɗan daga irin ƙalubalen da take fuskanta a harkokin gudanarwar ta.

Pillars, ta wallafa ƙalubalen ne kamar haka, “A yanzu haka zancan da muke muku Kano Pillars ta rasa kudin da za taje garin Aba, domin buga wasan hamayya na Nigeria Premier league wato Zobia Classic”.

Wasan dai shine wasa mafi ɗaukar hankali a league din Nigeria baki ɗaya, ku taya mu yadawa dan Allah.

Continue Reading

Wasanni

Glesner ya zama sabon mai horas da Palace.

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace ta sanar da nadin Oliver Glesner a matsayin sabon mai horaswar ta.

Glesner wanda tsohon mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Eintracht Frankfurt ne mai shekaru 49 dan asalin kasar Austrian, ya maye gurbin tsohon mai horaswa Roy Hodson, wanda ake ganin ya gaza kai kungiyar ga tudun mun tsira.

A wasanni 16 da Crystal Palace ta buga a bayan nan ta yi rashin nasara a wasanni 10 duk karkashin jagorancin Roy Hodson wanda hakan yasa take mataki na 16 a teburin gasar firimiyar kasar Ingila.

Glesner dai ya rattaba kwantaragi da Palace har na tsawon shekaru biyu, zai kuma jagoranci kungiyar a wasan sa na farko da kungiyar kwallon kafa ta Burnley a ranar Asabar mai kamawa.

Continue Reading

Trending