Connect with us

Labarai

Tsoron zagi ya sanya ba ma shiga harkokin al’ummar Arewa – Ali Nuhu

Published

on

Fitaccen jarumin fina-finan Hausa a masana’antar Kannywood Ali Nuhu ya ce, tsoron yin shishshigi ko kuma zagi a dandalin sada zumunta ya sanya ba sa shiga cikin wani al’amari da ya shafi al’umma.

Ali Nuhu ya bayyana hakan ne a zantawar sa da gidan rediyon Dala a yau Juma’a.

Ya na mai cewa, “Mu na son shiga cikin al’amuran amma duba da gudun wulakanci mu ke kauda kai, kuma abubuwa da yawa na taimakon al’umma ‘yan Kannywood suna shiga domin bayar da tallafin su”. A cewar Ali Nuhu.

Ƴan wasan kwaikwayo da mawaƙa a yankin kudancin ƙasar nan dai ana ganin sun taka muhimmiyar rawa yayin zanga-zangar neman rusa rundunar ƴan sandan SARS, kuma wannan ba shi ne farau ba da in al’amuran al’umma sun tashi a yankin, mawaƙa da ƴan Film kan taka rawa wajen kawo sauyi ba.

Sai dai kuma a yankin mu na Arewa ba kasafai, mawaƙa ke shiga a dama da su kan al’amuran jama’a ba.

Itama dai jarumar fina-finan Kaddywood Saratu Gidado Daso ta ce, “Kyamar ‘yan fina-finan Hausa ya sanya ba ma shiga cikin al’amuran da suka shafi al’umma, mu da ba’a damu ba ta yaya za mu fito wata zanga-zanga”. Inji Saratu Gidado Daso.

 

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending