Labarai
#SecureNorth: Mun gaji da salon mulkin Buhari – ‘Yan Najeriya
Ƴan Najeriya sun fara kosawa da salon mulkin gwamnatin kasar da suka ce ta yi biris da sha’anin tsaro.
Wannan na zuwa ne yayinda al’amauran tsaro a arewacin kasar ke kara tabarbarewa, a dai-dai lokacin da alhinin mutuwar manoma 43 da ake zargin mayakan Boko Haram ne suka yi musu yankan rago a jihar Borno.
Al’ummar kasar dai na ganin munin matalsar tsaro na kara ci musu tuwo a kwarya, lamarin da ya sanya da dama daga cikin al’ummar kasar suka fusata, inda suke bayyana ra’ayoyinsu a kafafen sada zumunta.
An Hausa Man is my Brother
An Hausa Woman is my SisterAn Igbo is my brother
An Igbo woman is my sisterA Yoruba man is my brother
A Yoruba woman is my sister. #BuhariMustGo #BUHARIrESIGNnOW#BuhariMustGo #EndNaijaKillings pic.twitter.com/cv0M3A6hOL— OmOLUABI ToRI ANU GBA (@Heavenpikin) November 30, 2020
The insecurity in Nigeria and the new level of hardship are all indications that Buhari and APC have failed Nigerians, they should do the honorable thing and fuck off !!! Dem just sit down dey collect loans wtf ?! 🤬🇳🇬🤮#SackTheServiceChiefs #BuhariResignNow #EndSARS pic.twitter.com/uiGfffTKvW
— Livingstone 🦍 (@TripleOGLstone) November 30, 2020
Abinda kuma ke yawo a kafafenn sada zumunta baya ga batun sai Buharin ya sauka daga mulkin kasar, shine batun a sallami hafsoshin tsaro, akan abinda ‘yan Najeriya ke cewa sun gaza magance matsalar tsaro da ke kara kamari musamman, a arewacin kasar.
Haka zalika al’ummar Najeriya sun ce shugaban ya gaza cika musu alkawuran da ya dauka a lokacin da yake neman kujerar shugabancin kasar, a yayinda tsadar rayuwa ke ci musu tuwo a kwarya.
Nothing to see here, Just #SackTheServiceChiefs or #BuhariResignNow pic.twitter.com/GMhcESXxBw
— 😷 (@Yusuf_A_J) November 30, 2020
Buhari promised us all dis back in 2015 and now he is killing us..#BuhariResignNow#EndBadGovernmentInNigeria#SackTheServiceChiefs#BuhariMustGo pic.twitter.com/WAzyWyS5wj
— Akinyode Taiwo (@taiwo1989) November 30, 2020
Yanzu haka dai hankulan mazauna arewa maso yamma da ke fama da matsalar fashi da makami da kuma garkuwa da mutane a tashe yake, yayinda mazauna yankin arewa maso gabashin kasar ke cikin tashin hankali.
Tun bayan yankan ragon da aka yiwa manoma a kauyen Zabarmari na jihar Borno ne, hankulan jama’a ya kara karkata, yayinda ake ganin mazauna arewacin kasar na cikin tashin hankali, sakamakon tabarbarewar tsaro.
43 innocent farmers where brutally killed by Boko Haram. We’re not safe in this country @MBuhari doesn’t care about the killings in the north. We’re tired, we need action now, we can’t tolerate it anymore
Buhari please Resign for our peace😭
#ZabarmariMassacre #BuhariResignNow— PRINCESS ZARAH👸 (@XahraBKumbo) November 28, 2020
Rundunar sojin Najeriya ta ce har yanzu ana neman wasu daga cikin mutanen da harin ya rutsa da su, yayin da wasu ƴan ƙasar ke ganin ko shugaba Muhammadu Buhari ya tashi tsaye wajen magance matsalar tsaron ko kuma ya sauka daga mulki.
Me ke faruwa a Arewa maso Yamma?
Wani rahoto da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar ya ce manoma 110 ne aka kashe a Zabarmari na jihar Borno, ba 43 ba kamar yadda hukumomin tsaron kasar suka ce.
Majalisar ta bayyana wannan harin a matsayin abu mafi muni da aka yiwa fararen hula, cikin shekarar 2020 a duniya.
A dai-dai lokacin da ake zaman makokin mutuwar manoman ne, kuma rikici ya balle a jihar Kaduna da ke Arewa maso Yammacin Najeriya, inda rahotanni suka tabbatar da mutuwar mutum bakwai, sai kananan yara da suka tsere bayan da wasu na daban suka jikkata.
Bayan kwana guda da barkewar rikicin ne, wasu ‘yan bindiga suka tare hanyar Zaria zuwa garin Kaduna, inda suka jikkata mutane, ko da yake kawo yanzu ba a tabbatar da mutuwar ko da mutum guda ba.
Labarai
Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa
An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.
Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.
Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.
Hangen Dala
Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano
A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.
Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.
Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.
Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.
Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.
Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito
Labarai
Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure
Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.
Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.
Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.
Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.
-
Nishadi4 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Manyan Labarai4 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai4 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya2 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai4 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi4 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su