Connect with us

Labarai

#SecureNorth: Mun gaji da salon mulkin Buhari – ‘Yan Najeriya

Published

on

Ƴan Najeriya sun fara kosawa da salon mulkin gwamnatin kasar da suka ce ta yi biris da sha’anin tsaro.

Wannan na zuwa ne yayinda al’amauran tsaro a arewacin kasar ke kara tabarbarewa, a dai-dai lokacin da alhinin mutuwar manoma 43 da ake zargin mayakan Boko Haram ne suka yi musu yankan rago a jihar Borno.

Al’ummar kasar dai na ganin munin matalsar tsaro na kara ci musu tuwo a kwarya, lamarin da ya sanya da dama daga cikin al’ummar kasar suka fusata, inda suke bayyana ra’ayoyinsu a kafafen sada zumunta.

Abinda kuma ke yawo a kafafenn sada zumunta baya ga batun sai Buharin ya sauka daga mulkin kasar, shine batun a sallami hafsoshin tsaro, akan abinda ‘yan Najeriya ke cewa sun gaza magance matsalar tsaro da ke kara kamari musamman, a arewacin kasar.

Haka zalika al’ummar Najeriya sun ce shugaban ya gaza cika musu alkawuran da ya dauka a lokacin da yake neman kujerar shugabancin kasar, a yayinda tsadar rayuwa ke ci musu tuwo a kwarya.

Yanzu haka dai hankulan mazauna arewa maso yamma da ke fama da matsalar fashi da makami da kuma garkuwa da mutane a tashe yake, yayinda mazauna yankin arewa maso gabashin kasar ke cikin tashin hankali.

Tun bayan yankan ragon da aka yiwa manoma a kauyen Zabarmari na jihar Borno ne, hankulan jama’a ya kara karkata, yayinda ake ganin mazauna arewacin kasar na cikin tashin hankali, sakamakon tabarbarewar tsaro.

Rundunar sojin Najeriya ta ce har yanzu ana neman wasu daga cikin mutanen da harin ya rutsa da su, yayin da wasu ƴan ƙasar ke ganin ko shugaba Muhammadu Buhari ya tashi tsaye wajen magance matsalar tsaron ko kuma ya sauka daga mulki.

Me ke faruwa a Arewa maso Yamma?

Wani rahoto da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar ya ce manoma 110 ne aka kashe a Zabarmari na jihar Borno, ba 43 ba kamar yadda hukumomin tsaron kasar suka ce.

Majalisar ta bayyana wannan harin a matsayin abu mafi muni da aka yiwa fararen hula, cikin shekarar 2020 a duniya.

A dai-dai lokacin da ake zaman makokin mutuwar manoman ne, kuma rikici ya balle a jihar Kaduna da ke Arewa maso Yammacin Najeriya, inda rahotanni suka tabbatar da mutuwar mutum bakwai, sai kananan yara da suka tsere bayan da wasu na daban suka jikkata.

Bayan kwana guda da barkewar rikicin ne, wasu ‘yan bindiga suka tare hanyar Zaria zuwa garin Kaduna, inda suka jikkata mutane, ko da yake kawo yanzu ba a tabbatar da mutuwar ko da mutum guda ba.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending