Connect with us

Labarai

PDP – Bashir Sanata ya zama jami’in hulda da jama’a

Published

on

Jam’iyar PDP a jihar Kano ta nada Bashir Aminu V.I.O wato Bashir Sanata a matsayin sabon jami’in hulda da jama’a na jam’iyar.

Zaben wanda ya gudana a yau Litinin a Lugard dake unguwar Nasarawa GRA wanda a ka zabi, Alhaji Shehu Sagagi a matsayin shugaban jami’yar, yayin da Dankaka Hussaini Bbebeji ya zama mataimakin jam’iyar.

Ga jerin zababbin sunayen ‘ya’yan jam’iyar kamar haka:

1- Alh. Shehu Sagagi

Chairman

  1. Hon. Dankaka Hussaini Bebeji

Deputy Chairman

  1. Hon. Hamisu Saad Dogonnama

Vice Chairman Kano Central

  1. Hon. Hashim Sulaiman Dungurawa

Vice Chairman Kano North

  1. Hon. Mukhtar Dankadai

Vice Chairman KanoSouth

  1. Hon. Jamilu Abubakar Danbatta

Secretary

  1. Hon.Yusuf Ibrahim Abubakar

Assistant Secretary Kano Central

  1. Hon. Jamilu Garba Garo

Asistant Secretary Kano-North

  1. Hon. Abba Abubakar Wudil

Assistant Secretary Kano-South

  1. Hon Idris Zare Rogo

Treasurer

  1. Hon. Sani Gora

Assistant Treasurer Kano-Central

  1. Hon. Magaji Uba Yalwa

Assistant Treasurer Kano-North

  1. Hon. Umar Maigoro Rano

Assistant Treasurer Kano-South

  1. Hon. Dahiru Maitama Arrow

Financial Secretary

  1. Hon. Auwal Garko

Assistant Financial Secretary

  1. Hon. Bashir Sanata

P.R.O

  1. Haj. Bintoto Kofar Ruwa

Assistant P.R.O

  1. Hon. Sunusi Surajo Kwankwaso

Organizing Secretary

  1. Hon. Adamu Ali Ibrahim

Asst. Organizing Sec. Kano-South

  1. Hon. Ismail Sabo Abba

Asst. Organizing Sec. Kano-Central

  1. Hon. Abubakar Sulaiman Mairogo

Asst. Organizing Sec. Kano-North

  1. Barr. Wangida Isah

Legal Adviser

  1. Barr. Amina Umar Garba

Assistant Legal Adviser

  1. Hajiya Halima Uba Jalli

Women Leader

  1. Mariya Sani Karaye

Assistant Women Leader Kano-South

  1. Haj. A’isha Jafaru Fagge

Assistant Women Leader Kano-Central

  1. Haj. Aina’u Muhammad Bichi

Assistant Women Leader Kano-North

  1. Hon. Hafizu Sharif Gambo

Youth Leader

  1. Hon. Nura Ali Doguwa

Assistant Youth Leader Kano-South

  1. Hon. Kabiru Haruna Getso

Assistant Youth Leader Kano-South

  1. Hon. Shamsu Aliyu Samanja

Assistant Youth Leader Kano-Central

  1. Hon. Auwalu Nagero

Auditor

  1. Haj. Atine Abdullahi

Assistant Auditor

  1. Rabiu Sarkin Fulani

Ex-officio

  1. Faruk Gwadabe

Ex-officio

  1. Sabo Yau Yaura

Ex-officio

  1. Haj. Habiba Abdullahi Takai

Ex-officio

  1. Hajiya Mama Dorayi

Ex-officio

  1. Haj. Balaraba Sani Lawan Bagwai

Ibrahim Adam

Wakilin mu Abba Haruna ya tabbatar mana da cewa tuni sababbin jagororin jam’iyar su ka fara aiki nan take har zuwa tsawon shekaru hudu a nan gaba.

Labarai

Kisan gillar Edo: A gaggauta nemawa mutanen da aka kashe haƙƙin su, ko mu ɗauki Mataki bisa doka – Human Rights

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Global Community for Human Rights Network, ta buƙaci gwamnatin tarayya da ta Kano da kuma ta jihar Edo, da gaggauta neman haƙƙin Mafarautan nan ƴan asalin jihar Kano waɗanda aka yi wa kisan gilla a garin Uromi na jihar Edo.

Daraktan ƙungiyar na ƙasa Kwamared Gambo Madaki shi ne ya bayyana wa tashar Dala FM Kano, hakan a ranar Litinin, lokacin da yake tsokaci kan kisan sama da Mafarauta 16 a jihar Edo, waɗanda suka taho daga jihar Ribas za su dawo gida Kano.

Ya ce baya ga ɗaukar matakin lalubo waɗanda suka aikata rashin imanin, akwai buƙatar a ɗauki mummunan mataki akan su don daƙile afkuwar irin hakan a gaba.

Rahotanni sun bayyana cewa wasu ɓatabgari ne su ka damke wadanda abin ya shafa a Uromi da ke karamar hukumar Esan ta Arewa maso Gabas ta Jihar Edo, inda su ka ga bindigogin farauta, sai kawai su ka yanke cewa ai masu garkuwa da mutane ne, inda suka kona su da ransu a ranar Alhamis.

Lamarin dai ya jawo cece-ku-ce, inda ‘yan Najeriya da dama ke zargin gwamnati da gazawa wajen dakile irin wannan ɗaukar doka a hannu.

A cewar Gambo Madaki, baya ga batun kafa kwamiti da gwamnatin Kano ta yi akan wannan batun, ya kamata gwamna Abba Kabir Yusuf ya ƙara bibiyar lamarin da kan sa, don ganin an ɗauki matakin da ya dace akan kisan gillar ko kuma su ɗauki mataki bisa doka.

Continue Reading

Labarai

Mun baza jami’an mu lungu da saƙo don samar da tsaro yayin bikin Sallah a Kano – Anty Snaching Phone

Published

on

Rundunar tsaron nan da ke yaƙi da faɗan Daba da ƙwacen Waya da kuma dakile Shaye-shayen kayan maye, ta Anty Snaching Phone, ta ce ta baza jami’an ta kusan dubu ɗaya da za su shiga lungu da saƙo na jihar nan, domin samar da tsaro a yayin bukukuwan ƙaramar Sallah.

Kwamandan rundunar a nan Kano Inuwa Salisu Sharaɗa ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da Freedom Radio, ya kuma ce jami’an su za su yi duk mai yiyuwa wajen daƙile ayyukan ɓata garin da ke shirin tayar da hankalin al’umma yayin bikin sallar.

“Daga cikin jami’an mu da za su samar da tsaron akwai na cikin kayan mu da kuma na farin kaya, kuma sun fara bazama guraren da mu ka tura su tun cikin kin daren Asabar ɗin nan kuma za su yi aiki cikin ƙwarewa kamar yadda suka samu horo, “in ji Inuwa”.

Sharaɗa, ya kuma ce hakan na cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar Kano ƙarkashin jagorancin gwamna Abba Kabir Yusuf, bisa kulawar shugaban kwamitin karta-kwana da ke yaƙi da miyagun ɗabi’u da gwamnan ya kafa ƙarkashin Dakta Yusuf Ƙofar Mata.

Wannan dai na zuwa ne yayin da za’a gudanar da sallar Idi, ta ƙaramar Sallah a ranar Lahadin nan a Najeriya, da Jamhuriyyar Nijar da ƙasar Saudiyya, da ma wasu ƙasashen Duniya.

Continue Reading

Labarai

Za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 – Masani

Published

on

Wani masanin ilmin Taurari da ke jihar Kano a arewacin Najeriya, Mallam Nasir Falaki Al-Kanawi, ya ce za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 saboda watan Shawwal ba zai ganu ba a ranar Asabar, don da ƙarfe 11:58 na safe za a haifi jinjirin watan kuma zai faɗi 06:48 na Yamma.

Mallam Nasiru Alfaki Al-Kanawi ya bayyana hakan ne a wani taƙaitaccen jawabi da ya yi wa gidan rediyon Dala FM Kano a ranar Juma’a 28 ga watan Maris ɗin shekarar 2025.

Alfalaki ya kuma ce watan zai faɗi ne da ƙarfe 6:48 na yamma mintuna kasa da 10 kenan bayan faduwar Rana, kasancewar ranar ƙarfe 6:37 na yamma za ta fadi.

Ya ci gaba da cewa to wannan dalilin ne zai sa watan ba zai ganu ba, ko da kuwa da Na’ura ne kasancewar bai samu wadataccen hasken da zai ɗosana daga ranar ba, wanda aƙalla yana buƙatar awanni 13 zuwa 16 daga haifeshi kafin ace an iya ganinsa, Allah shi ne mafi sani Mai iko akan komai.

Continue Reading

Trending