Labarai
PDP – Bashir Sanata ya zama jami’in hulda da jama’a
Jam’iyar PDP a jihar Kano ta nada Bashir Aminu V.I.O wato Bashir Sanata a matsayin sabon jami’in hulda da jama’a na jam’iyar.
Zaben wanda ya gudana a yau Litinin a Lugard dake unguwar Nasarawa GRA wanda a ka zabi, Alhaji Shehu Sagagi a matsayin shugaban jami’yar, yayin da Dankaka Hussaini Bbebeji ya zama mataimakin jam’iyar.
Ga jerin zababbin sunayen ‘ya’yan jam’iyar kamar haka:
1- Alh. Shehu Sagagi
Chairman
- Hon. Dankaka Hussaini Bebeji
Deputy Chairman
- Hon. Hamisu Saad Dogonnama
Vice Chairman Kano Central
- Hon. Hashim Sulaiman Dungurawa
Vice Chairman Kano North
- Hon. Mukhtar Dankadai
Vice Chairman KanoSouth
- Hon. Jamilu Abubakar Danbatta
Secretary
- Hon.Yusuf Ibrahim Abubakar
Assistant Secretary Kano Central
- Hon. Jamilu Garba Garo
Asistant Secretary Kano-North
- Hon. Abba Abubakar Wudil
Assistant Secretary Kano-South
- Hon Idris Zare Rogo
Treasurer
- Hon. Sani Gora
Assistant Treasurer Kano-Central
- Hon. Magaji Uba Yalwa
Assistant Treasurer Kano-North
- Hon. Umar Maigoro Rano
Assistant Treasurer Kano-South
- Hon. Dahiru Maitama Arrow
Financial Secretary
- Hon. Auwal Garko
Assistant Financial Secretary
- Hon. Bashir Sanata
P.R.O
- Haj. Bintoto Kofar Ruwa
Assistant P.R.O
- Hon. Sunusi Surajo Kwankwaso
Organizing Secretary
- Hon. Adamu Ali Ibrahim
Asst. Organizing Sec. Kano-South
- Hon. Ismail Sabo Abba
Asst. Organizing Sec. Kano-Central
- Hon. Abubakar Sulaiman Mairogo
Asst. Organizing Sec. Kano-North
- Barr. Wangida Isah
Legal Adviser
- Barr. Amina Umar Garba
Assistant Legal Adviser
- Hajiya Halima Uba Jalli
Women Leader
- Mariya Sani Karaye
Assistant Women Leader Kano-South
- Haj. A’isha Jafaru Fagge
Assistant Women Leader Kano-Central
- Haj. Aina’u Muhammad Bichi
Assistant Women Leader Kano-North
- Hon. Hafizu Sharif Gambo
Youth Leader
- Hon. Nura Ali Doguwa
Assistant Youth Leader Kano-South
- Hon. Kabiru Haruna Getso
Assistant Youth Leader Kano-South
- Hon. Shamsu Aliyu Samanja
Assistant Youth Leader Kano-Central
- Hon. Auwalu Nagero
Auditor
- Haj. Atine Abdullahi
Assistant Auditor
- Rabiu Sarkin Fulani
Ex-officio
- Faruk Gwadabe
Ex-officio
- Sabo Yau Yaura
Ex-officio
- Haj. Habiba Abdullahi Takai
Ex-officio
- Hajiya Mama Dorayi
Ex-officio
- Haj. Balaraba Sani Lawan Bagwai
Ibrahim Adam
Wakilin mu Abba Haruna ya tabbatar mana da cewa tuni sababbin jagororin jam’iyar su ka fara aiki nan take har zuwa tsawon shekaru hudu a nan gaba.
Labarai
Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa
An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.
Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.
Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.
Hangen Dala
Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano
A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.
Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.
Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.
Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.
Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.
Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito
Labarai
Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure
Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.
Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.
Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.
Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.
-
Nishadi4 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Manyan Labarai4 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai4 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya2 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai4 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi4 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su