Connect with us

Labarai

Jam’iyyar PDP ta dakatar da ‘dan takarar gwamnan Kano

Published

on

Jam’iyyar PDP ta dakatar da tsohon ɗan takarar gwamnan Kano Ibrahim Al’amin Little na tsawon wata guda.

Sakataren yaɗa labaran jam’iyyar PDP na ƙaramar hukumar Nassarawa Sulaiman Mustapha Mainasara ne ya tabbatar da hakan a tattaunawar sa da Dala FM.

A cewar sa, shugabancin mazaɓar Tudunwada ne ya aike musu da takardar dakatarwar bisa zarginsa da aikata laifukan da suka saɓa da kundin tsarin mulkin jam’iyya.

Ana zargin Little da tsame kansa daga al’amuran jam’iyya sannan ya kai jam’iyyar ƙara kotu, ba tare da yin ƙorafi ga jam’iyya ba, sannan ana zarginsa da yiwa jam’iyyar zagon ƙasa a cewar Mainasara.

Har kawo lokacin haɗa wannan rahoto Alhaji Al’amin Little bai ce komai ba a kai.

Wannan rikici na cikin gida, abu ne da ya dabaibaye jam’iyyar PDP a Kano, ko a makon da ya gabata ma, tsagin Ambasada Aminu Wali ya sanar da korar tsohon gwamna Kwankwaso daga jam’iyyar.

Sai dai tsagin Kwankwaso ya yi watsi da korar da aka yi masa.

Yayin da ake rikicin shugabanci tsakanin ɓangarorin biyu, uwar jam’iyyar ta ƙasa ta ce tsagin Kwankwaso su ne halastattun shugabannin jam’iyyar.

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Trending