Connect with us

Labarai

Rediyon Dala ta na baiwa matasa gudunmawa – Kungiyar masoya Dala

Published

on

Shugaban Ƙungiyar masoya tashar Dala FM Kano Mansur Tallman mai Faci, ya bayyana gida gidan rediyon Dala a matsayin gidan da yake bada gudunmawa ga al’umma musamman ma matasa.

Mansur Tallman ya bayyana hakan ne jim kaɗan bayan tashi daga taron sada zumunci da suka shirya tare da ma’aikatan tashar da kuma masu sauraron tashar, wanda ya gudana a Lahadin makon da ya gabata a makarantar Ɗandago dake yankin karamar hukumar Gwale a jihar Kano.

Yana mai cewa, “Babu shakka gidan rediyon Dala FM Kano, ya yi fice wajen wa’azantarwa, faɗakarwa, harma da Nishaɗantar da al’umma, shiyasa muka ƙirƙiri Ƙungiya ga masu sauraron tashar domin ƙara ƙarfafa zumunci a tsakanin”.

Ya kuma ce, “Mun karrama ma’aikatan tashar ne bisa yadda suke ƙoƙari wajen ilmantar da al’umma a yayin gudanar da aikinsu”. A cewar Mansur Tallman.

Da yake nasa jawabin shugaban tashar Dala FM Kano Mallam Ahmad Garzali Yakubu, wanda ya samu wakilcin ɗaya daga cikin ma’aikatan tashar Munnirat Sule Garko, miƙa godiyarsa ya yi ga shugabannin Ƙungiyar harma da dukkanin masu sauraren tashar bisa samun damar halartas taron da sukayi, inda yace yana alfahari da dukkanin masu sauraron tashar ta Dala FM Kano.

A yayin taron dai Ƙungiyar ta karrama wasu daga cikin ma’aikatan tashar Dala FM Kano, waɗanda suka haɗar da Tijjani Adamu, Munnirat Sule Garko, Abdulƙadir Yusif Gwarzo, da kuma Muhammad B Umar Hankaka, da dai sauran wasu ma’aikatan, harma da wasu daga cikin masu sauraron tashar.

Wakilin mu da ya halarci taron Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa, Al’umma da dama ne suka halarci taron daga sassa daban daban na jihar Kano, harma da wasu jahohin ƙasar nan, da suka hadar da Jihar Legas, Katsina, Harma da Jigawa da dai sauransu.

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Labarai

Iyaye ku dai ma marawa ƴaƴan ku baya akan abinda suke yi da ya saɓawa doka – Mai unguwar Ja’en Jigawa

Published

on

Mai unguwar Ja’en Jigawa da ke ƙaramar hukumar Gwale a jihar Kano Sani Muhammad, ya ce bai kamata a rinƙa samun wasu iyaye da ɗabi’ar nan ta marawa ƴaƴan su baya akan abinda yaran suke aikatawa na saɓawa Doka, domin gujewa abinda ka je ya dawo.

Mai unguwar ya bayyana hakan ne yayin zantwarsa da gidan rediyon Dala FM, a lokacin da yake tsokaci kan yadda ake samun wasu daga cikin iyayen yankin sa na marawa ƴaƴan su baya kan abinda suke yi na ba dai dai ba, lamarin da yake ƙara ƙara kangarar da tarbiyyar ƴaƴan tare da tayar da hankalin al’umma.

Mai unguwa Sani Muhammad, ya kuma ce matuƙar yaran ba za su zauna lafiya a cikin unguwa da al’umma ba, to kuwa za su rinƙa ɗaukar matakin miƙa yaran hannun jami’an tsaro mafi kusa, domin ɗaukar matakin da ya dace a kan su, wajen ganin sun sauke nauyin da aka ɗora musu.

Sani Muhammad, ya ƙara da cewa ko a baya bayan nan wasu matasa sai da suka yi yunƙurin yin abinda bai kamata ba, lamarin da yasa aka ɗauki mataki a kansu amma aka samu wasu daga cikin iyaye suka marawa yaran nasu baya, wanda hakan kan haifar da barazanar tsaro.

Continue Reading

Labarai

Matasa ku ƙara dagewa da neman Ilmin addini da na zamani – Dr. Abdallah Gadan Kaya

Published

on

Fitaccen malamin addinin Musluncin nan Dakta Abdallah Usman Umar, ya shawarci matasa da su ƙara mayar da hankali wajen neman ilmin addinin da na zamani, domin zama ababen koyi a tsakanin al’umma.

Dakta Abdallah Gadan Ƙaya, ya bayyana hakan ne ta cikin Tafsirin Al-ƙur’ani mai girma, da yake gabatarwa cikin wannan watan azumin Ramadana a jihar Gombe.

A cewar sa, “Akwai buƙatar matasa ku yi riƙo da ƙananan sana’o’in dogaro da kai, da za ku rinƙa biyawa kan ku kuɗin makaranta wajen neman ilimi domin kaucewa zama a cikin jahilci, “in ji shi”.

Dakta Abdallah, ya kuma yi kira ga shugabanni da su dukkan abinda ya dace wajen inganta makarantu a sassan ƙasar nan, domin ganin ɗalibai sun samu ingantaccen Ilmi.

Continue Reading

Trending