Ilimi
Rahoto: Zanga-zanga mu ka yi ba yajin aiki ba – BUK

Ma’aikatan jami’ar Bayero a jihar Kano, sun kasance a cikin jerin ma’aikatan jami’o’in Nijeriya a kan wata zanga-zangar lumana da su ka gudanar a safiyar ranar Talata.
Gamayyar manyan ma’aikatan da kanana na SANU da kuma NASU ne su ka gudanar da Zanga-zangar a harabar sabuwar jami’ar Bayeron a jihar Kano.
Wakilin mu Ibrahim Abdullahi Sorondinki ya halarci wajen zanga-zangar ya aiko mana rahoto daga jami’ar.
Ilimi
Ba za mu janye komawa makaranta ba a Kano – Kwamishinan Ilimi

Gwamnatin jihar Kano, ta tabbatar da gobe Litinin 18-01-2021 za a koma makarantu a fadin jihar baki daya.
Cikin wata sanarwa da Kwamishinan ilimi, Muhammad Sunusi Kiro ya fitar da sanarwar, cewa gwamnatin Kano za ta bude dukannin makarantun Firamare da kuma Sakandire a jihar Kano.
Ya kuma ce”Iyayen Yara da su mayar da ‘ya’yan su wadanda suke makarantun kwana a ranar Lahadin nan da mu ke ciki, gobe kuma daliban jeka ka dawo za su koma makaranta, sannan duk wani labarai da yake zagayawa cewa ba za a koma makaranta ba a gobe, zancan ba shi da tushe balle makama. Gwamnatin jihar Kano ba ta da niyar janyewa komawa makaranta a gobe”. A cewar Muhammad Sunusi Kiru.
Ilimi
SHASA: An gwangwaje kungiyar dalibai da kyautar Mota

Sabon shugaban kungiyar daliban unguwar Sharada dake karamar hukumar birni a jihar Kano, Bukhari Isa Sa’id, ya ce ya shirya tsaf domin sauke nauyin da ya rataya a wuyan shi ga daliban yankin Sharada.
Jawabin shugaban kungiyar, Bukhari, na zuwa ne a lokacin da a ka rantsar da shi a jiya Lahadi, karkashin masu fada a ji dake yankin da kuma jihar Kano.
Ya kuma ce zai yi iya kokarin shi wajen ciyar da dukannin dalibai gaba, musamman ma a bangaren koyo da koyarwa a yankin Sharada.
Yayin taron dai wani attajiri yi wa kungiyar alkawarin kyautar Mota kyauta domin su tafikar da kungiyar a unguwar Sharada.
Ga abun da ya ke cewa da bakin shi.
Ilimi
Ko matashi ya san waye shi a cikin al’umma?

Na’ibin masallacin juma’a na Masjid Umar Sa’id Tudun Wada dake harabar gidan rediyon manoma a yankin unguwar Tukuntawa dake karamar hukumar birni a jihar Kano, Gwani Fasihu Gwani Dan Birni, ya ce cikakken matashi shi ne mutumin da a ka sanshi ya tashi cikin bautar Allah maimakon wata tabara da za a tsince shi a ciki.
Ya ce”“Matashi shi ne ginshikin kowace al’umma, idan sun gyaru to al’umma ta gyaru, kuma matashi shi ne jigon rayuwa ya na bukatar a ja shi a jiki a na yi masa nasiha a lokacin da aka tsince shi ya na wani abu da bai dace ba, sannan matashi ya tsaya ya yi karatun ta nutsu domin saita rayuwar sa a turbar mun tsira, idan mu ka kalli Sahabai duk matasa ne Annabawa matasa ne, saboda haka dole ne matashi ya tsaya ya yi aikin Allah wajen yin karatun alkur’ani da yin biyayya ga na gaba da shi tare da bayar da gudunmawa a cikin al’umma”.
Wakilin mu Tijjani Adamu wanda ya halarci sallar juma’a a masallacin ya rawaito mana cewa cikin hudubar Liman Gwani Fasihu Gwani Dan Birni ya mayar da hankali ne a kan matashi dungurugum a cikin hudubar Limamun.
-
Manyan Labarai11 months ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Nishadi1 year ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai11 months ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Nishadi1 year ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai12 months ago
Ba’amurkiya da masoyin ta sun hada cinkoso a kasuwar Sabon Gari
-
Nishadi1 year ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su
-
Labarai3 months ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Manyan Labarai12 months ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
You must be logged in to post a comment Login
You must log in to post a comment.