Connect with us

Labarai

Zaben kananan hukumomi: NBC ta gargadi ‘yan Jarida

Published

on

Hukumar kula da Kafafen yaɗa labarai ta ƙasa NBC, ta gargadi ‘yan Jarida da su kasance masu bin dokoki yayin gudanar da zaɓen kananan hukumomi da za’a yi a ranar Asabar 16-01-2021 mai zuwa a jihar Kano.

Daraktan hukumar mai kula da shiyyar Kano da Kaduna, Alhaji Abubakar Kumo ne ya bukaci hakan yayin ziyarar da ya kawo gidan rediyon Dala FM a ranar Laraba.

Yana mai cewa, “Matuƙar ‘yan Jarida, za su ƙara ƙaimi wajen bin dokoki a yayin gudanar da zaɓen, za’a ƙara samun ci gaba a fannin yaɗa labarai yayin gudanar da zaɓen”.

Ya kuma ce, “Babban maƙasudin kawo ziyarar shi ne, domin hukumar ta ƙara tunatar da ma’aikatan gidan, domin bin dokoki a yayin gudanar da ayyukan su musamman a lokutan zabe”. Inji Alhaji Abubakar Kumo.

Da yake nasa jawabin, mataimakin shugaban rukunin gidajen Freedom Radio, Adamu Ism’ila Garki, godiya ya yi da ziyarar da hukumar ta kawo, tare da kira ga kungiyoyin dake da hurumi cewa da su rinka kula da abubuwan dake faruwa a shafukan sada zumunta.

Wakiliyar mu Nafisa Isah Adam ta rawaito cewar, shugaban tashar Dala FM, Ahmad Garzali Yakubu ya ce sun karbi ziyarar hannu bibbiyu kuma suna fatan ci gaba da kulla alaka tsakanin hukumar ta NBC da kuma rukunin gidajen Radiyon.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending