Connect with us

Labarai

Masarutar Karaye ta nada Kwankwaso a matsayin Makaman Karaye

Published

on

Mai martaba Sarkin Karaye, Alhaji Dr Ibrahim Abubakar na II ya nada Alhaji Saleh Musa Saleh Kwankwaso a matsayin Makaman Karaye hakiman gundumar Madobi tare da wasu hakimai guda hudu.

Sauran hakiman da akwai Alhaji Ibrahim Sani Gaya a matsayin Sarkin Shanun Karaye hakimin Shanono kuma Dan majalisar Sarki da Alhaji Sidi Mustapha Karaye a matsayin Dan masanin Karaye kuma Dan majalisar Sarki. Yayin da a ka nada Alhaji Bashir Mai kudi Aminu da Alhaji Ahmad Muhammad Tudun Kaya a mukaman San Turaki da Shattiman Karaye.

Kafin nada sabon Makaman na Karaye har ila yau Danmajalisar Sarki kuma daya daga cikin masu zabar Sarki na masarautar ta Karaye.

Da yake jawabi yayin nadin, Mai Martaba Sarkin Karaye Alhaji Dr Ibrahim Abubakar II ya ce“Ku kasance masu biyayya da kuma ci gaba da bada gudunmawa domin tabbatar da ci gaban masarautar”.

Cikin sanarwar da Haruna Gunduwawa wanda shi ne babban Jami’ in yada labarai na masarautar Karaye ya sanyawa hannu ta ce mataimakin Gwamnan Jihar Kano Dr. Nasiru Yusuf Gawuna tare da tawagar gwamnatin jihar Kano ne suka samu damar halartar taron nadin.

Alhaji Dr Ibrahim Abubakar II ya kuma godewa Gwamna Abdullahi Umar Ganduje bisa kokarin shi na samar da managarciyar ruyuwa al’ umma. Sannan ya kuma sake jaddada bukatar shi ga Gwamnatin da ta gaggauta kammala aikin hanyar da ta shi daga Janguza ta tafi Kabo ta kuma zarce Karaye, domin amfanin al’ummar Masarautar.

Dr. Ibrahim Abubakar II ya ce”Wannan hanya na da makukar amfani wajen habaka tattalin arzikin al’ummar yanki, kuma ita ce hanya mafi sauri wajen zuwa birnin Kano daga Karaye”.

 

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Trending