Connect with us

Labarai

Masarutar Karaye ta nada Kwankwaso a matsayin Makaman Karaye

Published

on

Mai martaba Sarkin Karaye, Alhaji Dr Ibrahim Abubakar na II ya nada Alhaji Saleh Musa Saleh Kwankwaso a matsayin Makaman Karaye hakiman gundumar Madobi tare da wasu hakimai guda hudu.

Sauran hakiman da akwai Alhaji Ibrahim Sani Gaya a matsayin Sarkin Shanun Karaye hakimin Shanono kuma Dan majalisar Sarki da Alhaji Sidi Mustapha Karaye a matsayin Dan masanin Karaye kuma Dan majalisar Sarki. Yayin da a ka nada Alhaji Bashir Mai kudi Aminu da Alhaji Ahmad Muhammad Tudun Kaya a mukaman San Turaki da Shattiman Karaye.

Kafin nada sabon Makaman na Karaye har ila yau Danmajalisar Sarki kuma daya daga cikin masu zabar Sarki na masarautar ta Karaye.

Da yake jawabi yayin nadin, Mai Martaba Sarkin Karaye Alhaji Dr Ibrahim Abubakar II ya ce“Ku kasance masu biyayya da kuma ci gaba da bada gudunmawa domin tabbatar da ci gaban masarautar”.

Cikin sanarwar da Haruna Gunduwawa wanda shi ne babban Jami’ in yada labarai na masarautar Karaye ya sanyawa hannu ta ce mataimakin Gwamnan Jihar Kano Dr. Nasiru Yusuf Gawuna tare da tawagar gwamnatin jihar Kano ne suka samu damar halartar taron nadin.

Alhaji Dr Ibrahim Abubakar II ya kuma godewa Gwamna Abdullahi Umar Ganduje bisa kokarin shi na samar da managarciyar ruyuwa al’ umma. Sannan ya kuma sake jaddada bukatar shi ga Gwamnatin da ta gaggauta kammala aikin hanyar da ta shi daga Janguza ta tafi Kabo ta kuma zarce Karaye, domin amfanin al’ummar Masarautar.

Dr. Ibrahim Abubakar II ya ce”Wannan hanya na da makukar amfani wajen habaka tattalin arzikin al’ummar yanki, kuma ita ce hanya mafi sauri wajen zuwa birnin Kano daga Karaye”.

 

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending