Connect with us

Labarai

GWAMNATIN KENYA TA SOMA TUHUMAR MANYAN JAMI’ANTA DA AKE GANIN SUN FI KARFIN DOKAR KASAR

Published

on

Gwamnatin kasar Kenya ta soma tuhumar manyan jami’anta da ake ganin sun fi karfin dokar kasar, a wani bangare na kokarin da ta keyi wajen yaki da cin hanci da rashawa a kasar.
A cikin wannan satin ne gwamnatin kasar Kenya ta tuhumi wasu manyan jami’an ta biyu da suke jin sun fi karfin doka.
Ana dai tuhumar wadannan jami’an ne da laifin cin hanci da rashawa na zunzurutun kudi har dala miliyan 3 na ginin hanyar jirgin kasar da wani kanfanin kasar China ke ginawa a kasar ta Kenya.
Wannan tuhumar na manyan jami’an, wata manuniya ce ga gwamnatin Uhuru Kenyata cewa, ba wani jami’in gwamnati da ya fi karfin doka a yakin da gwamnatin ke yi da cin hanci da rashawa.
Sai dai masu sharhi akan al’amurran yau da kullun suna fata wannan tuhumar za ta kai ga gurfanar dasu har a kai ga yanke musu hukunci, wanda hakan zai zamo abin tarihi da gwamnatin ta Kenyata za ta bari ko kuma yakasance barazana ga ‘yan siyasar kasar.
Rahotanni dai sun ce ana tuhumar babban darektan kanfanin jirgin kasa na kasar Atanas Maina da shugaban hukumar kula da albarkatun kasar Mohammed Swazuri, su ake tuhuma da laifin aringizon dala miliyan biyu na biyan kudin diyya.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending