Connect with us

Labarai

Iyaye su ƙara mayar da hankali kan karatun ‘ya’yan su – Ibni Sina

Published

on

Babban Kwamandan hukumar hisbah ta jihar Kano Sheikh Harun Muhammad Sani Ibn Sina, ya bukaci iyayen yara da su kara mayar da hankali wajen kulawa da karatun ya’yansu.

Sheikh Harun Ibn Sina ya bayyana hakan ne, ta bakin kwamandan hisbah na karamar hukumar Kumbotso Gwani Murtala Mahmud, wanda ya wakilci babban kwamanda hisbar a yayin saukar karatun Alqur’ani mai girma, da makarantar Naftahurrahman fitta’alim wa kira’atul Qur’an ta gudanar cikin unguwar Sheka Baranda unguwar Fulani dake karamar hukumar kumbotso na dalibai sittin maza goma mata hamsin.

Ya ce, “Kamata ya yi iyaye su fi mayar da hankali ga ilmin addini ga ‘ya’yansu, maimakon fifiko da suke nunawa a bangaren karatun boko”.

Da yake nasa jawabin, shugaban makarantar Gwani Muhammad Muhammad, jan hankalin masu hannu da shuni da kuma gwamnati ya yi, da su kara himma wajen tallafawa makarantar da abinda ya sawwaka, domin kai makarantar ga gaci.

Wakilin Abdulkadir Muhammad Sani Tukuntawa ya rawaito mana cewa, taron ya samu halartar manyan baki daga sassa daban daban, daga ciki kuwa akwai Yariman Kano Alhaji Lamido Abubakar bayero, da kuma shugaban ma’aikata Na yankin karamar hukumar kumbotso Wanda ya wakilici shugaban karamar hukumar kumbotso.

 

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending