Connect with us

Labarai

CPC Kano: An kama lalatacciyar Dusar Dabbobi motar Tirela 4

Published

on

Hukumar kare hakkin mai saye da mai sayarwa ta jihar Kano ta kama lalatacciyar dusar dabbobi kimanin motar tirela hudu da  kuma buhu dari bakwai da saba’in da hudu na gurbataccen takin zamani.

Mai rikon shugabancin hukumar Dakta Baffa Babba Dan Agundi ne ya sanar da haka ga manema labarai ta cikin wata takarda mai dauke das a hannun jami’in hulda da hukumar Musbahu Aminu Yakasai,ta bakin babban mataimaki na musamman ga gwamna a hukumar KAROTA Nasiru Usman Na’ibawa a ofishin sa.

Sanarwar ta kuma ce,  hukumar ta samu nasarar kama wasu kayayyakin amfanin  yau da kullum kimanin katan dubu biyu wadanda su ke gurbatattu da kuma wanda wa’adin amfaninsu ya kare.

Kayayyakin sun hada da magunguna da Taliyar makaroni da Man shafawa da na girki da Ganyen Shayi da abubuwan hada lemo da sauran su.

Ya ce, “An samu nasarar kame kayayyakin daga ranar Juma’a zuwa Litinin din da suka gabata a sakamakon rahotanni da aka samu daga wasu masu kishin jihar Kano da kuma sumame da ake kai wa kasuwanni”.

Shugaban ya ja hankalin ‘yan kasuwa masu irin wannan dabi’a ta sayarwa da al’umma kaya marasa kyau da su ji tsoron Allah musamman a wannan wata mai alfarma da ake neman gafara a wajen Ubangiji.

Hukumar kuma ta rufe wasu wuraren sayar da abinci daban-daban sakamakon rashin takardun shaidar gwajin lafiya ta ma’aikatan su da kuma rashin takardar shaidar wajen kasuwanci.

Wuraren sun hada da gidajen sayar da abinci da na sayar da ruwa da madarar Yoghout da sauransu.

 

 

 

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending