Connect with us

Labarai

Zargi: Matashin da ya addabi mutanen Goron Dutse ya shiga hannu

Published

on

Daga unguwar Yalwa dake yankin Goron Dutse, layin Ƴan Kaɗi bayan gidan malam Nasidi Abubakar, a karamar hukumar Dala, wani matashi mai suna Saddiqu mai laƙanin (mai idon) , a zargin sa da addabar al’ummar yankin da sace-sace, har ma a makon da ya gabata a ke zargin ya gayyato wasu guggun matasa daga wasu unguwannin suka farwa mutanen yankin da sara da suka har ma da satar wayoyi da kudi.

Abba Abubakar matashi ne mai shekaru ashirin (20) da haihuwa, kuma shi ne wanda a ke zargin an sara a lokacin da ɓata garin su ka shiga unguwar, ya ce “Ban san hawa ba ban san sauka ba, sai ji na yi an hau ni da sara lamarin da ya sa na gudu babu shiri, har kuma na shiga wani gida, amma saboda an sare ni a hannu na kasa rufe gidan da na shiga, saboda haka ina kira ga mahukunta a bi min hakki na”.A cewar matashi Abba.

Haka zalika wasu matasan da a ka bayyana cewa, ɓata garin sun rutsa da su har cikin shagon da su ke kwana, su ma mun zanta da mahaifin su, Alh Danlami Abubakar Goron Dutse, wanda ya ce, “Matasan ɗauke da muggan makamai sun yi kokarin shiga har inda ƴaƴa na su ke kwana, da yaran su ka kula, su ka shiga bandakin cikin dakin, su ka bar wayoyin su da kudi har Naira dubu sittin,  kuma mu na yabawa jami’an tsaro da wannan ƙoƙarin na su”. Inji Danlami.

Idris Abubakar Idris wanda a ka fi sani da Babangida ɗan Malam ya ce, “Mun ji daɗi da ya shiga hannu, saboda ya na addabar mu da yawan sace-sace“.

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Trending