Connect with us

Labarai

A kara rubanya kokarin da a ken a hidimtawa marayu – Dagacin Dabai

Published

on

Dagacin unguwar Dabai dake karamar hukumar Gwale, Malam Sanusi Ahmad Dahiru, ya hori daidaikun kungiyoyi ma su zaman kan su da su kara rubanya kokarin da su ke na hidimtawa marayu a yankunan su.

Malam Sanusi Ahmad Dahiru, ya bayyana hakan ne a yayin da wata cibiya mai suna Al-Infaq Foundation ta raba kayan salla ga marayu a unguwar Dabai a karshen makon da ya gabata.

Ya ce”Ina kira ga shugabannin kungiyoyin da ma ‘ya’yan kungiyar cewa, kar su gajiya a kan irn wannan aikin alherin da su ke gudanarwa”. Inji Malam Sanusi.

yabawa wata kungiyar taimakon kai da kai mai suna Al-Infaq Foundation dake unguwar Dabai bisa yadda tayi hobbasa wajen tallafawa marayu da kuma marasa karfi dinkakkun kayan salla

A jawabin shi, Kwamrade Salisu Alhassan wanda ya kasance shugaban kungiyar, ya ce“Dama ita wannan kungiya, an kafata ne domin taimakon marasa karfi, ba wai mun kafa ta ba ne domin ‘yan siyasa ba”.

Sa dai kuma, Alhaji Sani Adam mai Alewa, shugaban kungiyar cigaban unguwar Dabai da kewayan ta, cewa ya yi”Kamata ya yi al’umma, su rinka kwatanta marayu a matsayin ‘ya’yan su, saboda kowa zai iya kasan cewa a wannan matsayin”.

Wakilin mu Nasir Khalid Abubakar ya rawaito cewa, kungiyar Al-Infaq ta rabawa marayu da mabukata kayan Sallah dinkakku a yankin na Dabai.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending