Connect with us

Labarai

Tsaiko: Abduljabbar ya zargi gwamnatin Kano a kan shari’a

Published

on

A yau Laraba 28-07-2021, babbar kotun shari’ar muslinci ta birni a jihar Kano ta ci gaba da sauraron Shari’ar nan wadda gwamnatin Kano ta gurfanar da Malam Abduljabbar Nasiru Kabara.

Gwamnatin ta na zargin malamin da laifin batanci ga fiyayyen halitta Annabi Muhammadu (S.A.W).

A zaman kotun na yau mai Shari’a Ibrahim Sarki Yola, ya tambayi lauyan gwamnati cewar a zaman da kotun ta yi a baya wanda a ke tuhuma ya musanta zargin da ake masa, domin haka ko kun zo da shaidun.

A nan ne lauyar gwamnati ta shaidawa kotun cewar ba su zo da shaidun ba, domin suna bukatar su rubuta tuhuma daga ma’aikatar Shari’a tun da yanzu takarda tuhuma ta ‘yansanda ce kawai a gaban kotun.

A nan ne lauyan da ya ke kare Abduljabbar, Barrister Sale Muhammad Bakoro, ya bayyana wa kotun cewar masu kara suna son kawo tsaiko tunda Wanda ake Kara ya na tsare a gidan gyaran hali yau kwanaki 12 kenan, amma a ce har yanzu ba su shirya takarda tuhuma ba.

Saboda haka barrister Sale Bakoro ya roki kotun a kan cewar in har kotun za ta daga zaman, to kotun ta umarci masu kara su basu duk wasu takardu da su ka shafi Shari’ar da sunan shaidun da kuma duk wani abu wanda zai taimakawa wanda ake tuhuma, domin kare kansa.

A nan ne lauyar gwamnati ta bayyanawa kotun cewar lauyan wanda ake kara ya yi azarbabi dama duk wannan roke-roke da ya yi munsan su kuma da zarar mun gabatar da tuhuma zai ga mun kawo duk abubuwan da ya roka, domin haka ta jaddada rokonta akan a sanya wata rana.

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Trending