Connect with us

Labarai

Tsaiko: Abduljabbar ya zargi gwamnatin Kano a kan shari’a

Published

on

A yau Laraba 28-07-2021, babbar kotun shari’ar muslinci ta birni a jihar Kano ta ci gaba da sauraron Shari’ar nan wadda gwamnatin Kano ta gurfanar da Malam Abduljabbar Nasiru Kabara.

Gwamnatin ta na zargin malamin da laifin batanci ga fiyayyen halitta Annabi Muhammadu (S.A.W).

A zaman kotun na yau mai Shari’a Ibrahim Sarki Yola, ya tambayi lauyan gwamnati cewar a zaman da kotun ta yi a baya wanda a ke tuhuma ya musanta zargin da ake masa, domin haka ko kun zo da shaidun.

A nan ne lauyar gwamnati ta shaidawa kotun cewar ba su zo da shaidun ba, domin suna bukatar su rubuta tuhuma daga ma’aikatar Shari’a tun da yanzu takarda tuhuma ta ‘yansanda ce kawai a gaban kotun.

A nan ne lauyan da ya ke kare Abduljabbar, Barrister Sale Muhammad Bakoro, ya bayyana wa kotun cewar masu kara suna son kawo tsaiko tunda Wanda ake Kara ya na tsare a gidan gyaran hali yau kwanaki 12 kenan, amma a ce har yanzu ba su shirya takarda tuhuma ba.

Saboda haka barrister Sale Bakoro ya roki kotun a kan cewar in har kotun za ta daga zaman, to kotun ta umarci masu kara su basu duk wasu takardu da su ka shafi Shari’ar da sunan shaidun da kuma duk wani abu wanda zai taimakawa wanda ake tuhuma, domin kare kansa.

A nan ne lauyar gwamnati ta bayyanawa kotun cewar lauyan wanda ake kara ya yi azarbabi dama duk wannan roke-roke da ya yi munsan su kuma da zarar mun gabatar da tuhuma zai ga mun kawo duk abubuwan da ya roka, domin haka ta jaddada rokonta akan a sanya wata rana.

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Labarai

Iyaye ku dai ma marawa ƴaƴan ku baya akan abinda suke yi da ya saɓawa doka – Mai unguwar Ja’en Jigawa

Published

on

Mai unguwar Ja’en Jigawa da ke ƙaramar hukumar Gwale a jihar Kano Sani Muhammad, ya ce bai kamata a rinƙa samun wasu iyaye da ɗabi’ar nan ta marawa ƴaƴan su baya akan abinda yaran suke aikatawa na saɓawa Doka, domin gujewa abinda ka je ya dawo.

Mai unguwar ya bayyana hakan ne yayin zantwarsa da gidan rediyon Dala FM, a lokacin da yake tsokaci kan yadda ake samun wasu daga cikin iyayen yankin sa na marawa ƴaƴan su baya kan abinda suke yi na ba dai dai ba, lamarin da yake ƙara ƙara kangarar da tarbiyyar ƴaƴan tare da tayar da hankalin al’umma.

Mai unguwa Sani Muhammad, ya kuma ce matuƙar yaran ba za su zauna lafiya a cikin unguwa da al’umma ba, to kuwa za su rinƙa ɗaukar matakin miƙa yaran hannun jami’an tsaro mafi kusa, domin ɗaukar matakin da ya dace a kan su, wajen ganin sun sauke nauyin da aka ɗora musu.

Sani Muhammad, ya ƙara da cewa ko a baya bayan nan wasu matasa sai da suka yi yunƙurin yin abinda bai kamata ba, lamarin da yasa aka ɗauki mataki a kansu amma aka samu wasu daga cikin iyaye suka marawa yaran nasu baya, wanda hakan kan haifar da barazanar tsaro.

Continue Reading

Labarai

Matasa ku ƙara dagewa da neman Ilmin addini da na zamani – Dr. Abdallah Gadan Kaya

Published

on

Fitaccen malamin addinin Musluncin nan Dakta Abdallah Usman Umar, ya shawarci matasa da su ƙara mayar da hankali wajen neman ilmin addinin da na zamani, domin zama ababen koyi a tsakanin al’umma.

Dakta Abdallah Gadan Ƙaya, ya bayyana hakan ne ta cikin Tafsirin Al-ƙur’ani mai girma, da yake gabatarwa cikin wannan watan azumin Ramadana a jihar Gombe.

A cewar sa, “Akwai buƙatar matasa ku yi riƙo da ƙananan sana’o’in dogaro da kai, da za ku rinƙa biyawa kan ku kuɗin makaranta wajen neman ilimi domin kaucewa zama a cikin jahilci, “in ji shi”.

Dakta Abdallah, ya kuma yi kira ga shugabanni da su dukkan abinda ya dace wajen inganta makarantu a sassan ƙasar nan, domin ganin ɗalibai sun samu ingantaccen Ilmi.

Continue Reading

Trending