Connect with us

Labarai

WANDA AKE ZARGIN DA DAUKAN HOTON BIDIYON GWAMNAN KANO YA CE ZAI BAYYANA A GABAN KWAMITIN DA KE BINCIKEN AL’AMAMARIN IDAN GWAMNAN MA ZAI ZO

Published

on

Mutumin da ake zargin ya dauki hoton bidiyon dake nuna gwamna Abdullahi Umar Ganduje yana karbar daloli daga hannun’yan kwangila, ya ce zai bayyana a gaban kwamitin dake bunciken al’amarin matukar shima Gandujen zai zo da kansa ba sakoba.
Hakan dai na kunshe ne cikin wata wasika da lauyan mai fallasar, Barista Sa’idu Muhammad Tudun Wada, ya aikewa da kwamitin na majalissar dokoki, yana mai cewa, a yayin zaman a gayyaci masana harkar hoto mai motsi daga hukumar S.S da kuma wani masanin daga kasar waje da kuma Jafar-Jafar sai kuma sheik Aminu Ibrahim daurawa.
Lauyan mai fallasar ya kuma ce, a yayin zaman a kawo dukanin faya-fayan bidiyon, harma da wadanda ba a saki ba, shi kuma zai kawo dukkanin muhimman abubuwan daya ya yi amfani dasu wajen daukar bidiyon, ciki harda kyamarar, tare da bada damar ayi masa tambaya daga daya zuwa goma, wadanda za’a mika masa su, kafin ya bayyana a gaban kwamitin.
Karin wani sharadin da lauyan mai fallasar ya bayar shi ne, wanda yake tsayawa zai yi badda bami fuska tare da boye sunansa, kuma zaman ya kasance da karancin mutane da kuma samun kariya daga hukumomi tsaro don kare rayuwarsa data iyalansa da kuma kasuwancinsa.
Acewar lauyan mai fallasar Sa’idu Muhammad Tudun Wada, Wanda yake tsayawa ya kuma bukaci da ya mika kwafin wasikar ga hukumomin, I.C.P.C da shugabannin kungiyoyin lauyoyi na kasa data ‘yan jaridu, sai kuma kungiyar Amnesty mai kare hakkin dan adam da tabbatar da daidaito a ayyukan gwamnati da hukumomi, sai kuma ta karshe kungiya mai tabbatar da hakokin zamantakewa dana tattalin arziki da bin diddigi.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending