Connect with us

Labarai

KSCPS: An kama sinadarin wanke hannu mara inganci a Kano

Published

on

Hukumar kare hakkin mai saye da mai sayarwa ta jihar Kano, ta kama kimanin katan Dubu Daya da Dari Biyar na sinadirin wanke hannu wato (Hand Sanitiser) a unguwar Birgade dake karamar hukumar Nassarawa.

Hukumar ta samu ruwan Haidrojin na wanke ciwo da Shanshanbale da jarkokin sinadarin hada wadannan abubuwa da dama a cikin rumbun ajiyar kayayyakin, wanda wani mutum ya tseguntawa hukumar labarin wajen.

Mai rikon shugabancin hukumar, Dr Baffa Babba Dan Agundi ne ya bayyana hakan, jim kadan bayan bayan kama kayan, wanda babban mataimaki na musamman ga gwamna a hukumar KAROTA, Nasiru Usman Na’ibawa ya wakilta.

Ya ce, “Dukkan kayayyakin wa’adin amfani da su ya kare, kuma ba sa dauke da lambar rajista ta NAFDAC, saboda haka hukumar ba za ta ragawa dukkan wanda ta samu da laifi ba”. A cewar Baffa Baffa.

Dan Agundi, ya kuma yi kira ga al’ummar jihar Kano, da su kasance masu  takatsantsan wajen yin amfani da irin wadannan magungunan, musamman ma a wannan lokaci na cutar COVID 19.

Labarai

NAHCON ta sanya ranar fara jigilar maniyyata aikin hajjin bana zuwa Saudiyya

Published

on

Yanzu haka hukumar Aikin Hajji ta ƙasa NAHCON, ta 15 ga watan nan na Mayun 2024, a matsayin ranar da za’a fara jigilar maniyyata aikin hajjin bana, zuwa ƙasa mai tsarki.

Bayanin hakan ya fito ne ta bakin shugaban hukumar ta NAHCON, Jalal Ahmad Arabi, a wajen taron masu ruwa da tsaki kan aikin Hajji da Umrah, da ya gudana yau Alhamis birnin tarayya Abuja.

“Maniyyata kimanin 65,500 ne za su sauke Farali daga ƙasar nan a ƙasa mai tsarki; za su shafe aƙalla kwanaki huɗu domin yin ziyara a Madina kafin fara aikin Hajji, “in ji Arabi”.

Daga bisani shugaban hukumar aikin hajjin Jalal Ahmad Arabi, ya kuma bayyana cewa za ayi jigilar maniyyata aikin hajjin ne daga cibiyoyi 10 a faɗi ƙasar nan.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Laraba a matsayin ranar hutu

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Laraba, 1 ga watan Mayun 2024, a matsayin ranar hutu, domin bikin ranar ma’aikata na wannan shekara.

Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hakan, a cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Talata.

Olubunmi, ya kuma sake nanata buƙatar ganin ma’aikata sun jajirce da yin aiki yadda ya kamata a dukkanib matakai daban-daban.

Continue Reading

Labarai

Wahalar Fetur ta haifar mana da koma baya a sana’ar mu – Mai Motar Haya

Published

on

Wani mai sana’ar tuƙin motar Haya, da kuma lodin fasinjoji mai suna Kabiru Muhammad, mazaunin ƙaramar hukumar Munjibir, ya ce ƙarancin motocin Haya da ake samu a yanzu, yana da alaƙa da wahalar man Fetur da ake fuskanta a sassan Najeriya.

A zantawar mutumin da wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il, ta cikin shirin rahotanni daga ƴan Zazu na yau Talata, ya ce a baya har motoci hamsin suke yiwa lodin fasinjoji su tashi, amma a yanzu Mota ɗaya suke iya cikawa sakamakon ƙarancin Fetur da ake fama da shi.

Ya kuma ce ƙaranci tare da tsadar man fetur ɗin da ake fama da shi, sun haddasa musu koma baya a sana’ar su, baya ga batun kuma matsalar da suke fuskanta da fasinjoji wajen biyan kuɗin Mota.

Wakiliyarmu da ta bibiyi shirin na ƴan Zazu Ummi Bala Ahmad ta rawaito cewa, matuƙin motar Kabiru Muhammad, ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta jahohi, da su yi abinda ya kamata dan ganin farashin man Fetur ɗin ya sauka, domin al’umma su samun sauƙi.

Continue Reading

Trending