Connect with us

Labarai

Kotu: Idan Aminu Attakawa ya tsere masu karbar beli za su biya Naira Miliyan 1

Published

on

Kotun majistret mai lamba 23 karkashin mai Shari’a, Sanusi Usman Atana ta tsayar da ranar 5 ga watan gobe, domin ci gaba da shari’ar da ‘Yansanda suka gurfanar da wani mutum mai, suna Aminu Ahmad Attakawa, wanda a ke zargin sa da laifin yunkurin tayar da hankalin al umma ta kafar yada labarai.

Kunshin tuhumar ya bayyana cewar a ranar 2 ga wata ne, Aminu Attakawa, ya je gidan wani rediyo ya bayyana cewar filayen da su ke unguwar Rimin Zakara mallakar Jami’ar Bayaro ne.

Kunshin zargin ya bayyana cewar wanda a ke tuhuma ya bayyana cewar ya na da shaidu na takardu da su ka nuna cewar filayen mallakar Jami’ar ne.

Hakan ne ya sanya wa su mazauna Rimin Zakara su ke da’awar filayen mallakin su ne su ka shigar da kara a kan wannan ikirari.

A zaman kotun na yau an karanta kunshin tuhumar, kuma magatakardar kotun, Inusa Sule Beli, shi ne ya fassara kunshin zargin sai dai Aminu Attakawa ya musanta. Kotun ta sanya shi a hannun beli bisa sharadin sai ya kawo mutum 2 daya fitaccen dan kasuwa dayan kuma mai matakin albashi na 15, an kuma umarce shi kar ya sake yin maganar ta kowace kafa har zuwa karshen Shari’ar. wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail, ya rawaito cewar kotun ta bayyana cewar idan, Aminun ya tsere masu karbar belin za su biya Naira miliyan daya.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending