Connect with us

Labarai

Kano: An samu hatsaniya tsakanin direbobin Tirela da KAROTA da Road Safety

Published

on

Safiyar Lahadi ne a ka samu wata hatsaniya tsakanin Direbobin Tirela da jami’an hukumar kiyaye afkuwar haɗura da na hukumar Karota a Sabon Titin Panshekara dake yankin ƙaramar hukumar Gwale, inda su ka rufe hanyar babu wucewa baki ɗaya a lokacin.

A zantawar wakilin mu Hassan Mamuda Ya’u da wani Direban Tirelan mai suna, Tasi’u Musa Yusuf, tare da wani Direba a wajen sun ce, sun rufe hanyar ne bisa zargin farfasa musu gilashi da cire lamba, da kuma cirewa wani Direba batir ɗin motarsa da jami’an hukumomin biyu su ka yi, inda Direbobin su ka ce ba za su buɗe hanyar ba, har sai an biya su ɓarnar da a ka yi musu.

A kan hakan ne wakilin namu ya tuntuɓi mai magana da yawun hukumar kiyaye afkuwar haɗura ta Road Safety ta jihar Kano, sai dai ya ce a jirawo za su bincika, haka shi ma mai magana da yawun hukumar Karota, Nabulisi Abubakar Ƙofar Na’isa ya ce zai bincika.

Kasancewar jami’an ‘ƴan sanda sun halarci wajen da al’amarin ya faru tare da kama wa su matasa da a ke zargi da farfasa gilashin motar jami’an hukumar kiyaye afkuwar haɗurar, hakan ne ya sa wakilin namu ya tuntuɓi Kakakin rundunar, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ta wayar tarho, sai dai har zuwa yanzu bamu same shi ba.

Motar da a ka fasa gilashin ta.

Direbobin dai sun rufe hanyar ne ta Panshekara daga ƙarfe 7 har zuwa karfe kusan 10:45 na safe, kamar yadda wakilin namu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito mana.

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Trending