Labarai
Dakarun tsaftar muhalli: An baiwa hammata iska da mai sayar da abinci

Hatsaniyar ta kaure ne tsakanin dakarun tsaftar muhalli na jihar Kano da wata mata mai sayar da abinci a unguwar Kabuga.
Ma’aikatan kula da tsaftar muhalli sun dai shiga gidan sayar da abinci ne domin duba yadda tsaftar muhallin wajen, wanda a ka yi zargin ma’aikatan gidan abinci su ka farwa ma’aikatan da duka, har su ka yagawa guda daga cikin ma aikatan riga.
Wakilin mu Mu’azu Musa Ibrahim ya tuntubi jagorar tafiyar na dakarun tsaftar muhallin ya ce”Mun iske gidan sayar da abincin kaca-kaca babu tsafta, wanda ma’aikatan gidan sayar da abincin su ka fara zagin mu, mu kuma mun fada mu su ga yadda za su gyara, kawai sai ji mu ka yi sun fara dukan mu”. Inji Kwamrade Sadiku Muhammad Wada.
Wakilin mu ya tuntubi bangaren ma su sayar da abincin, amma sun ki cewa komai a kai, sakamakon lamarin na wajen ‘yansanda, ya kuma tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce za su bincika.

Baba Suda
NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.
Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.
A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.
Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Labarai
Real Madrid ta kaddamar da Alexander

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid ta ƙaddamar da ɗan wasa Trent Alexander Arnold a yau a matsayin ɗan wasan ta
Inda shugaban ƙungiyar Flerontino Perez yace yau suna matuƙar Farin ciki kasancewar sun mallaki babban ɗan wasan baya a duniya.
Shima ɗan Wasa Arnold ya bayyana cewa yana cikin farin ciki kuma mafarkin sa ya cika na zama ɗan Wasan Madrid a yau.

Daurin Boye
Zan shiga kawancen ‘yan jamiyyar hamayya – tsohon Minista

Tsohon ministan sufurin Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce a shirye yake don shiga ƙawancen ƴan jamiyyar hamayya domin ƙalubalantar Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027
A wata hira da BBC, tsohon gwamnan na jihar Rivers ya ce suna ƙoƙarin samar da haɗakar siyasar da za ta samar da sauyi a ƙasar.
Amaechi wanda ɗan jam’iyyar APC ne ya nuna damuwa kan abin da ya ƙira halin ƙuncin rayuwa da ƙasar ke ciki.
Amaechi ya ce bai cire tsammanin yin takarar shugaban ƙasa ba, illa lokaci ne kawai zai tantance.

-
Nishadi6 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi6 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su