Connect with us

Labarai

Kotu ta tura wani mutum zuwa gidan gyaran hali saboda cin amana

Published

on

Wani mutum mai suna, Isma’il Muhammad Zangon Dakata ya gurfana a gaban kotun shari’ar musulunci da ke zaman ta a PRP Kwana Hudu karkashin, Alkali Isa Rabi’u Gaya da tuhumar sa da cin amana d cuta, laifukan da su ka saba da sashi na 203 dana 206, na kundin tafikar da shari’ar musulunci na jihar Kano.

Kunshin tuhumar ya nuna cewa, wani mai suna Bashir Muhammad, dan garin Bidda ta jihar Naija ne ya ba shi a jiyar shinkafa samfafera buhu Dari Biyu da Hamsin, wanda kudin ya kai Naira Miliyan Uku da Dubu Dari da Hamshin, sai dai bayan dansanda mai gabatar da kara, Detective Aliyu Abidin Murtala ya karanta masa kunshin tuhumar ya amsa, amma dai ya ce miliyan Uku ya Sani.

Mai gabatar da kara ya roki kotun da ta bashi rantsuwar kore tuhuma a kan Dubu Dari Biyar din da ya ke musu, ta kuma amsa an kuma bashi rantsuwar a cikin kotun, Daga nan kuma kotun ta yi hukunci, inda a laifin farko na cin amana ta daure shi shekara Uku ko zabin biyan tarar NairaDubu Ashirin, laifin cuta kuma daurin shekara biyu ko tarar Naira Dubu Ashirin, sannan zai biya rankon Naira miliyan Uku.

Wakilin mu Abubakar Sabo ya rawaito cewa, kotun ta ce hukuncin daurin zai tafi ne a tare.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending