Connect with us

Wasanni

Ballon d’Or: Messi ya lashe ƙyautar gwarzon ɗan wasa karo na 7

Published

on

Dan wasan gaba na Paris St-Germain da kasar Argentina, Lionel Messi ya lashe kyautar gwarzon dan wasan kwallon kafa na duniya wato Ballon d’Or na bana a karo na bakwai.

Messi, mai shekaru 34, ya taimaka wa kasarsa ta lashe kofin Copa America, wanda ya zama lambar karramawa ta farko a duniya, kuma ya ci kwallaye 40 a kakar shekarar 2021 da 28 a Barcelona, Hudu a Paris St-Germain da Takwas a Argentina.

Dan wasan gaba na Bayern Munich da kasar Poland Robert Lewandowski ne ya zo na Biyu, dan wasan tsakiya na Chelsea da Italiya Jorginho ya zo na Uku sai dan wasan gaban Real Madrid na Faransa Karim Benzema ya zo na Hudu.
‘Yan jarida 180 ne suka kada kuri’ar Ballon d’Or daga ko’ina cikin duniya, duk da cewa ba a samu kyautar ba a shekarar 2020 saboda cutar Corona.

Ko dai Messi ko Cristiano Ronaldo sun lashe kyautar har sau Biyar ne a duk shekara daga 2008 zuwa 2019, baya ga 2018 da dan wasan tsakiya na Croatia, Luka Modric ya lashes au Daya.

Messi ya riga ya lashe kofin fiye da kowane dan wasa kuma nasararsa ta Bakwai ta zo ne bayan ya lashe a shekarar 2009, 2010, 2011, 2012, 2015 da kuma 2019.
Lewandowski ya zura kwallaye 53 a dukkan gasa a shekarar 2021 a Bayern kuma an ba shi kyautar gwarzon dan wasan gaba, sabuwar kyautar da aka sanar sa’o’i kadan kafin fara bikin.

Gianluigi Donnarumma na Paris St-Germain, wanda ya taimakawa Italiya lashe gasar Euro 2020, ya lashe kyautar Yashin Trophy a matsayin mafi kyawun mai tsaron gida, yayin da Chelsea ta lashe gasar zakarun Turai ta lashe kyautar kungiya mafi kyawun shekara.

Dan wasan tsakiya na Barcelona Pedri, mai shekaru 19, ya lashe Kopa Trophy a matsayin gwarzon dan wasa mai shekaru kasa da 21, inda ‘yan wasan Ingila Jude Bellingham, Mason Greenwood da Bukayo Saka suka zo na Biyu da na Biyar da na Shida.

‘Yan wasa 14 daga cikin 30 da aka zaba a matsayin Ballon d’Or a halin yanzu suna buga gasar Premier.

Wasanni

Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta 2023/2024.

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta shekarar 2023/2024, bayan da suka samu nasara a kan Weder Bremen da ci 5-0.

Hakan ne kuma ya kawo ƙarshen shekaru 11 da Bayern Munich, da ta yi tana lashe gasar.

Wannan dai shi ne karo na farko da Bayer Leverkusen suka taɓa lashe gasar a tarihi, ida suka gaza ɗaukar kofin a shekarar 2002 a ranar ƙarshe ta gasar.

Har ila yau, a dai wannan shekarar ne su kayi rashin nasara hannun Shalke 04, a wasan ƙarshe na German Cup Da ci 4-2.

Haka kuma, Real Madrid suka doke su a wasan ƙarshe na zakarun nahiyar turai.

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar bata taɓa ɗaukar wata gasa ba a ƙarni na 21, sai bayan da Xavi Alonso ya karɓe su.

Continue Reading

Wasanni

Hukumar NPFL, ta amince da buƙatar Kano Pillars na ɗage wasan ta na mako na 28 da Enyimba

Published

on

Yanzu haka an samu dai-daito da hukumar NPFL, wanda ta amince da bukatar Kano Pillars na dage wasanta na mako na 28, da Enyimba zuwa ranar Alhamis, mai zuwa.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, ce ta wallafa hakan a shafin ta na Facebook da yammacin Litinin ɗin nan, ta ce ƴan wasan ta za su tashi a gobe Talata, da safe zuwa Aba domin fafata wasannin su.

Idan dai ba’a manta ba ƙungiyar ta wallafa kaɗan daga irin ƙalubalen da take fuskanta a harkokin gudanarwar ta.

Pillars, ta wallafa ƙalubalen ne kamar haka, “A yanzu haka zancan da muke muku Kano Pillars ta rasa kudin da za taje garin Aba, domin buga wasan hamayya na Nigeria Premier league wato Zobia Classic”.

Wasan dai shine wasa mafi ɗaukar hankali a league din Nigeria baki ɗaya, ku taya mu yadawa dan Allah.

Continue Reading

Wasanni

Glesner ya zama sabon mai horas da Palace.

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace ta sanar da nadin Oliver Glesner a matsayin sabon mai horaswar ta.

Glesner wanda tsohon mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Eintracht Frankfurt ne mai shekaru 49 dan asalin kasar Austrian, ya maye gurbin tsohon mai horaswa Roy Hodson, wanda ake ganin ya gaza kai kungiyar ga tudun mun tsira.

A wasanni 16 da Crystal Palace ta buga a bayan nan ta yi rashin nasara a wasanni 10 duk karkashin jagorancin Roy Hodson wanda hakan yasa take mataki na 16 a teburin gasar firimiyar kasar Ingila.

Glesner dai ya rattaba kwantaragi da Palace har na tsawon shekaru biyu, zai kuma jagoranci kungiyar a wasan sa na farko da kungiyar kwallon kafa ta Burnley a ranar Asabar mai kamawa.

Continue Reading

Trending