Labarai
Kotu: Mu na nazari a kan wannan hukuncin – Ganduje

Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Ganduje, ya yi kira ga magoya bayansa a jam’iyyar APC mai mulki a jihar da su kwantar da hankalinsu tare da bin hanyar zaman lafiya da bin doka da oda.
Gwamnan ya yi wannan kiran ne a matsayin martani ga hukuncin da wata babbar kotun Abuja ta yanke ranar Juma’a, wanda ya nuna goyon bayan tsagin Malam Ibrahim Shekarau na G7 na jam’iyyar APC.
A wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar Kano, Muhammad Garba ya fitar, a ranar Juma’a, gwamnan ya ce” Tunda lamarin na cikin jam’iyya ne, gwamnati da jam’iyyar APC a halin yanzu muna nazari kan lamarin, domin samun mafita”.
Gwamna Ganduje ya kuma umurci jami’an tsaro da kada su lamunci rashin bin doka da oda, domin gwamnati ba za ta amince da duk wani aika-aika da ta’addanci ko tashin hankali a wani yanki na jihar ba, da sunan siyasa ko wani fage.
Sanarwar ta kuma nuna godiya ga ‘yan jam’iyyar a dukkan matakai da sauran masu ruwa da tsaki bisa jajircewar da su ka nuna wajen marawa jam’iyyar baya.
Labarai
Rahoto: Mu nisanci abinda Allah Ya hana domin samun saukin rayuwa – Limamin Tukuntawa

Limamin masallacin juma’a na Masjidul Kuba da ke unguwar Tukuntawa a jihar Kano, Malam Ahmad Ali, ya ce, al’umma su duba tsakanin su da Allah tare da nisantar abinda ya hana, domin saukin tsadar rayuwa.
Malam Ahmad Ali, ya bayyana hakan ne, yayin da yake yiwa wakilin mu na ‘yan Zazu, Ibrahim Abdullahi Soron Dinki, Karin bayani dangane da abinda hudubar da ya gabatar ta kunsa.
Akwai cikakken bayanin hudubar a muryar da ke kasa.
Labarai
Rahoto: Rubutu na da muhimmanci a mu’amalar bashi – Limamin Bompai

Limamin masallacin juma’a na Shelkwatar rundunar ‘yan sandan jihar Kano da ke unguwar Bompai, SP Abdulkadir Haruna, ya ce, akwai bukatar mu rinka gudanar da mu’amalar bashi yadda addinin musulunci.
SP Abdulkadir Haruna, yana bayyana hakan, a zantawarsa da wakilin mu na ‘yan Zazu, Abba Isah Muhammad, bayar idar da Sallar Juma’a.
Domin jin cikakken rahoton saurari wannan.
Labarai
Rahoto: Matashi ya yi yunkurin cinye tabar Wiwin da aka kama shi da ita a hanyar kotu

Ana zargin wani matashi ya yi yunkurin hadiye tabar Wiwi da miyagun kwayoyi da aka kama shi da ita a hanyar kotu.
Tunda fari jami’an tsaron, sun kama matasahin da zargin samun sa da kayan maye, inda yake boye da wasu basu sani ba, kafin kuma a kai shi kotu, ya ciro su yana yunkurin hadiye wa.
Wakilin mu na ‘yan Zazu, Ibrahim Abdullahi Soron Dinki yana da cikakken rahoton.
-
Nishadi3 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Manyan Labarai3 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai2 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Nishadi3 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai2 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Lafiya2 months ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Nishadi3 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su
-
Manyan Labarai3 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano