Connect with us

Labarai

Kotu: Mu na nazari a kan wannan hukuncin – Ganduje

Published

on

Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Ganduje, ya yi kira ga magoya bayansa a jam’iyyar APC mai mulki a jihar da su kwantar da hankalinsu tare da bin hanyar zaman lafiya da bin doka da oda.

Gwamnan ya yi wannan kiran ne a matsayin martani ga hukuncin da wata babbar kotun Abuja ta yanke ranar Juma’a, wanda ya nuna goyon bayan tsagin Malam Ibrahim Shekarau na G7 na jam’iyyar APC.

A wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar Kano, Muhammad Garba ya fitar, a ranar Juma’a, gwamnan ya ce” Tunda lamarin na cikin jam’iyya ne, gwamnati da jam’iyyar APC a halin yanzu muna nazari kan lamarin, domin samun mafita”.

Gwamna Ganduje ya kuma umurci jami’an tsaro da kada su lamunci rashin bin doka da oda, domin gwamnati ba za ta amince da duk wani aika-aika da ta’addanci ko tashin hankali a wani yanki na jihar ba, da sunan siyasa ko wani fage.

Sanarwar ta kuma nuna godiya ga ‘yan jam’iyyar a dukkan matakai da sauran masu ruwa da tsaki bisa jajircewar da su ka nuna wajen marawa jam’iyyar baya.

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.



Continue Reading

Labarai

Real Madrid ta kaddamar da Alexander

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid ta ƙaddamar da ɗan wasa Trent Alexander Arnold a yau a matsayin ɗan wasan ta

Inda shugaban ƙungiyar Flerontino Perez yace yau suna matuƙar Farin ciki kasancewar sun mallaki babban ɗan wasan baya a duniya.

 

Shima ɗan Wasa Arnold ya bayyana cewa yana cikin farin ciki kuma mafarkin sa ya cika na zama ɗan Wasan Madrid a yau.



Continue Reading

Daurin Boye

Zan shiga kawancen ‘yan jamiyyar hamayya – tsohon Minista

Published

on

Tsohon ministan sufurin Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce a shirye yake don shiga ƙawancen ƴan jamiyyar hamayya domin ƙalubalantar Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027

A wata hira da BBC, tsohon gwamnan na jihar Rivers ya ce suna ƙoƙarin samar da haɗakar siyasar da za ta samar da sauyi a ƙasar.

Amaechi wanda ɗan jam’iyyar APC ne  ya nuna damuwa kan abin da ya ƙira halin ƙuncin rayuwa da ƙasar ke ciki.

Amaechi ya ce bai cire tsammanin yin takarar shugaban ƙasa ba, illa lokaci ne kawai zai tantance.



Continue Reading

Trending