Connect with us

Labarai

Ta’aziyya: Kwankwaso ya magantu a kan Ganduje

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanat Rabi’u Musa Kwankwaso, abun farin ciki ne tare da murna, a lokacin da gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya kai masa ta’azziyar kaninsa.

Ya bayyana hakan ne a lokacin ganawa da BBC ya na mai cewa, ba wanda zai so ya bayar da gudunmawa wajen kafa jihar, ya kuma dawo ya ce ba ya son ta.

Ya ce”Na tabbata zuwan Ganduje wasu za su yi mamaki wasu kuma farin ciki, babban abun da na sa ni a lokacin wanda ya san wasu sun yi ba daidai ba ne kuma ya gyara, ina ganin ba wata matsala ba ce”.

“Ba mu tattauna a kan batun kasa ba, amma duk wanda ya tsinic kansa a siyasa ya zama wajibi ya ciyar da kasa gaba, duk wanda ya yi tafiya a baya ya zama wajibi ya fuskanci na daidai wanda ya san bai yi daidai ba sai ya gyara, kuma ko mai nene za a ji kuma za a gani”.

“Zuwan Ganduje abun farin ciki ne abun murna ne kuma abun jin dadi ne, mu muna siyasa domin ci gaban al’umma baki daya, ba ma yin siyasa domin gaba ko cin mutuncin wani ko kuma kece raini, saboda na tabbata wannan zuwan da Ganduje ya yi mutane za su yi farin ciki, amma wasu abubuwane wanda Allah ya sa alheri ne baki daya”. A cewar Kwankwaso.

Dr Rabi’u Musa Kwankwaso ya kuma godewa dukannin wadanda su ka yi masa ta’aziyyar kanin na sa.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending