Lafiya
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
An gano wani gida da ake ginawa a Unguwar Damfami a karamar hukumar Kumbotso da ake zargin ana cusa takardaun Kur’ani da Alluna da rubutu.
Al’ummar yankin, sun yi korafi kan ba za su bari a ci gaba da irin wannan ginin a cikin yankin su, saboda haka suke kubutar da aka kawo musu dauki.
Wakilin mu na ‘yan Zazu, Abba Isah Muhammad, na dauke da cikakken rahoton saurari wannan.
Baba Suda
Ƴan Nigeria miliyan 20 ne ke da taɓin-hankali – WHO
Wani rahoto da hukumar lafiya ta duniya, WHO, ta fitar ya ce ƴan Najeriya miliyan 20, daidai da kashi 20 cikin 100 na al’ummar kasar, na fama da matsalar taɓin-hankali.
Dr Azubike Aliche, Sakataren Kwamitin Amintattu na Cibiyar Kula da Lafiyar Ƙwaƙwalwa ta Najeriya-Amurka (NAIMH) ne ya bayyana haka a wani shirin horo kan lafiyar kwakwalwa da GAP Action da cibiyar su ka shirya a Owerri a jiya Talata.
Ya bayyana cewa “lamarin mai tayar da hankali ne” game da ciwon damuwa da ƴan Nijeriya ke fama da shi, wanda ya ce, ya kasance mafi girma a duniya kuma ya yi kira da a yi ƙoƙari matuƙa don canza yanayin.
“Rahotanni da ake samu sun nuna cewa kashi 10 cikin 100 na masu fama da tabin hankali ne kawai ke samun kulawa a Najeriya kuma dole ne a canza wannan yanayi,” in ji shi.
TRT Hausa
Lafiya
Kamilar Mace ce za ta iya hana ni yin shaye-shaye idan za ta aure ni- Ɗan Maye
Wani mai ta’ammali da kayan maye mai suna Abubakar Isah, ya ce idan ya samu mace Kamila mai hankali da tarbiyya wadda za ta aure shi, zai yi watsi da ta’ammali da kayan mayen.
A zantawar mutumin da wakilinmu na ‘yan Zazu Ibarahim Abdullahi sorondinki, ya ce ya kammala karatun sa na Digiri, kuma yana da ilimin addini bakin gwargwado, amma dole ta sanya shi yake ta’ammali da kayan mayen sakamakon rashin aikin yi.
Kazalika, mutumin ya ce bayan fatan ya haifi ɗan da zai zama irinsa, shi ya sa ma yake son ya samu mata ta gari wadda za ta bai wa ‘ya’yansa kyakkyawar tarbiyya ba irin tasa ba.
Lafiya
Likitocin da ke aiki da gwamnatin Kano sun jingine yajin aikin gargaɗin da suka fara
Likitocin da suke aiki da gwamnatin jihar Kano (NAGGMDP), sun jingine yajin aikin gargaɗin da suka fara a ranar Talata 01 ga watan Oktoban 2024, biyo bayan wani zama da su ka yi da kwamitin da gwamnatin ta kafa.
Sakataren ƙungiyar Dakta Anas Idris Hassan Shanno ne ya bayyana hakan ga manema labarai, jim kaɗan bayan kammala zaman gaggawa da su ka yi da ƴaƴan ƙungiyar.
Dakta Anas ya kuma ce sun ɗauki matakin jingine yajin aikin ne zuwa ƙarshen watan nan na 10, Kamar yadda gwamnatin ta dauki alkawarin cewa za ta biya masu buƙatun su a lokacin.
Wakilinmu Abubakar Sabo ya ruwaito cewa ƙungiyar ta kuma buƙaci dukkanin likitocin da ke ƙarƙashin ta da su koma bakin aikin su.
-
Nishadi6 years agoIna neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years agoHamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years agoMansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai6 years agoKAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai6 years agoAuren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Manyan Labarai6 years agoSabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi6 years agoAn gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su
-
Manyan Labarai6 years agoBa’amurkiya da masoyin ta sun hada cinkoso a kasuwar Sabon Gari
