Manyan Labarai
Liverpool ta amince Mane ya koma Bayern Munich

Liverpool ta amince da cinikin Yuro miliyan 41 kwatankwacin Fam miliyan 35.1, domin siyar da Sadio Mane ga zakarun gasar Bundesliga Bayern Munich.
Liverpool za su sami ƙayyadaddun Yuro miliyan 32 kwatankwacin Fam miliyan 27.4, tare da ƙarin Yuro miliyan 6 dangane da bayyanar da Yuro miliyan 3.
Liverpool ta yi watsi da tayin biyu daga Bayern kafin ta amince da sabon tayin dan wasan mai shekaru 30, wanda yarjejeniyarsa za ta kare har zuwa bazara mai zuwa.
Mane ya koma Liverpool kan fan miliyan 31 da kuma fam miliyan 2.5 daga Southampton a shekarar 2016.
Labarin tafiyar tasa ya biyo bayan sayan dan wasan gaban Uruguay, Darwin Nunez daga Benfica a ranar Talata kan fam miliyan 64.
Labarai
Gobara ta lalata dukiya ta miliyan 34 da asarar rayuka 135 a watan Yuni – Abdullahi

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano, ta ce, ta ceci rayuka 135 da dukiyoyi da kudinsu ya kai Naira miliyan 34.6 daga aukuwar gobara 42 a watan Yuni.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na hukumar,, PFS Saminu Abdullahi a Kano.
Abdullahi ya ce, mutane 24 ne suka mutu, sannan an kiyasta asarar dukiya ta Naira miliyan 13 da gobarar ta yi a lokacin.
A cewar sa, ma’aikatar ta amsa kiraye-kirayen ceto 77 da kuma kararrawar karya 17 daga mazauna jihar.
Ya danganta gobarar da rashin kula da amfani da na’urorin lantarki marasa inganci.
Ya shawarci jama’a da su rika kula, domin gujewa tashin gobara, yayin da bukukuwan Sallah ke gabatowa.
Abdullahi ya kuma bukace su da su rinka bin dokokin hanya domin gujewa hadurran mota yayin bikin.
Ilimi
Mataimakin Atiku a takarar shugaban kasa ya shaida wa INEC takardun WAEC dinsa sun bata

Rahotannin da muka samu cewa, dan takarar mataimakin shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Ifeanyi Okowa, ya sanar da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC, cewa takardar shaidar karatun sa na WAEC ta bata.
Okowa ya sanar da INEC game da batan shaidar takardun sa na ainihi a wani bangare na takardun sa na tsayawa takara a zaben 2023.
Ya ce, a cikin takardar shaidar hakan ya sa ya shiga ya kuma zana jarabawar kammala jarrabawar makarantar sakandare ta yammacin Afirka (WAEC) a shekarar 1974.
Sanarwar ta ce, ba za a iya samun ainihin takardar shaidar da aka bayar ba, in ji shi a cikin takardar.
Kamfanin dillancin labarai na kasa ya fahimci cewa, takardar sa ta asali ta fito ne daga babbar kotun shari’a ta jihar Delta da ke sashin shari’a na Asaba a ranar 3 ga Oktoba, 2006.
Ya kuma ce, “Cewa ni da kaina na yi rajista, kuma na zana jarrabawar kammala sakandare ta yammacin Afirka (WAEC) a shekarar 1974 a Kwalejin Edo da ke garin Benin a Jihar Edo a yanzu,” inji Gwamnan Jihar Delta. a cikin rantsuwar a cewar Tribune.
“Cewa na ci jarrabawar, sannan aka ba ni shaidar satifiket don haka. Cewa asalin takardar shaidar da aka ba ni yanzu ya ɓace, kuma ba a iya samunsa.
Ya kara da cewa, “Na yi wannan rantsuwar ne, saboda na sani kuma na yarda da hakan gaskiya ne, kuma bisa ga dokar rantsuwar jihar kamar yadda ta shafi jihar Delta,” in ji shi.
Labarai
Tsohon shugaban kasa Obasanjo ya dauki fasinjoji kyauta a Adaidaita Sahu

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya tuka babur mai kafa uku, inda ya debi fasinjoji kyauta.
Obasanjo, ya bi ta wasu hanyoyi a Abeokuta, babban birnin Ogun, don daukar fasinjoji, lamarin ya dauki hankulan mutane da dama wadanda su ka yi wa tsohon Shugaban kasa murna tare da daukar hotunan sa.
Obasanjo wanda ya rinka daukae mutane kyauta a ranar Asabar, ya zarce ta Moshood Abiola, NNPC Mega Station, Kasuwar Kuto, da dai sauransu.
Aikin wani bangare ne na shirin Keke na OBJ @ 85 na Cibiyar Bunkasa Matasa na Laburaren Shugaban Kasa na Olusegun Obasanjo (OOPL).
A cikin jawabinsa, Obasanjo ya yi kira ga matasa cewa kar su bar masu tada zaune tsaye.
Tsohon shugaban ya ce, duk da kalubalen da ake fuskanta, ya kamata su yi kokarin amfani da damar da ake da su domin yin tasiri ga al’umma.
“Dole ne matasa ku dunkule ku byar da gudummawa, domin ganin abubuwa su kasance kamar yadda ya kamata.
“Idan kun bar abubuwa ga masu yi muku almundahana sun cigaba da shugabanci, komai ba zai tafi daidai ba, domin ku ne shugabannin gobe, ba za ku taba samun haka gobe ba.
“Allah ya baka ikon zama abin da ke so ka zama. Idan kuka yanke shawara, Allah zai taimake ku ya samar da mutanen da za su taimake ku,” A cewra Obasanjo.
-
Nishadi3 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Manyan Labarai2 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai2 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Nishadi3 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai2 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Lafiya4 weeks ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Nishadi3 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su
-
Manyan Labarai2 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano