Manyan Labarai
Delegates 17 sun dawo mun da kudi na bayan sun ki zaba ta – Sanata Ibrahim

Dan majalisa mai wakiltan yankin Kwara ta tsakiya, Sanata Ibrahim Oloriegbe, ya ce, wasu wakilai wato Deligate da ya baiwa kudade a lokacin zaben fidda gwani na jam’iyyar sun mayar masa da kudaden sa.
Sanatan ya bayyana haka ne a lokacin da ya fito a gidan talabijin na Channels Television na shirin Sunrise Daily, inda ya yi magana kan rikicin da ke tsakanin jam’iyyar mai mulki.
Sanata Oloriegbe ya caccaki tsarin da aka gudanar da zabukan fidda gwanin da aka fi yi a jihohin da aka fi zargin gwamnonin da dora wakilai a kan magoya bayan jam’iyyar.
“Babu wani majalisa; kamar a jiha ta, gwamna kawai ya zabo su (delegates) da daddare ya ce, mun yi primaries sai jerin suka zo. Don haka, ba ku ma san su waye wakilan ba… kuma hakan ya faru a jihohi da yawa, ”in ji shi.
“Ko a inda ake zabar mutane, ya kamata a ba su ‘yancin yin amfani da ikonsu ta hanyar zaben wanda suke so, amma abin ba haka yake ba. Gwamnonin sun zabo wadanda za su ba su umarni kuma wasu daga cikinsu sun yi rantsuwar kada kuri’a a inda gwamnonin ke jagorantar su…haka kuma ya faru a jihar Kwara.
“A zabe na (na firamare), wakilai 17 ne suka dawo don ba ni kudi na da na ba su na kayan aiki; wasu kuma ba don sun ce ‘muna so mu zabe ku ba, amma ba a ba mu damar kada kuri’a ba. Akwai wani abokin aikina a Kogi wanda ya ambata cewa mutane sun dawo (don mayar da kudinsa).”
Dan majalisar na cikin wasu ‘yan jam’iyyar da dama a majalisar dattawa da suka rasa tikitin jam’iyyarsu na neman sake tsayawa takara a cikin majalisar dokoki.
Yayin da wasun su suka fice daga jam’iyyar APC, wasu kuma wadanda ba su ji dadin ci gaban da aka samu ba, sun gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari domin neman sa baki.

Manyan Labarai
Haihuwa a gida na janyo rasa rai – Dr. Hadiza Ashiru

Ƙwararriyar likitar Yara da ke asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano Dakta Hadiza Ashiru, ta shawarci mata masu juna biyu cewar, da zarar sun fara jin alamun Naƙuda su rinƙa hanzarin zuwa Asibiti, domin a basu agajin gaggawa, don gujewa fuskantar matsala ga lafiyar su.
Dr. Hadiza Ashiru, ta bayyana hakan yayin zantawar ta da tashar Dala FM Kano, a ranar Laraba 14 ga watan Mayun 2025.
Ta ce abin takaici ne yadda mace mai juna biyu take shafe tsawon lokaci tana zuwa Awo, amma idan Haihuwa ta zo mata take ƙauracewa zuwa Asibiti, lamarin da ta ce idan haihuwar ta zo da kuskure ana iya rasa ran macen, ta sha wahala daga ƙarshe a tafi da ita Asibiti babu shiri.
“Duk da aikin mu na likitanci da muke yi a Asibiti, amma a haka mu ke shiga lungu da saƙo muna wayar da kan mata domin faɗakar da su illar cutar sankarar bakin mahaifa, wadda ke haifar da yawaitar mutuwar su a yayin haihuwa, “in ji Dr. Hadiza”.
Har ila yau, likitar ta kuma ce, idan matsala ta faru da macen ana shan wahala wajen shawo kan matsalar, a don haka mata masu juna biyu su rinƙa zuwa Asibiti, domin su Haihu a can, don su samu wani sauƙi.

Manyan Labarai
Za ayi dokar da za ta tilastawa kamfanoni ɗaukar ma’aikata kashi 75 ƴan Kano – Gwamnati

A ƙoƙarin ta na ƙara samarwa Matasa aikin yi, gwamnatin jihar Kano ta sha alwashin yin dokar da za ta tilastawa kamfanoni masu zaman kansu ɗaukar kashi 75 cikin 100, na ma’aikata yan asalin jihar Kano.
Rahotanni sun bayyana cewa akan batun ne ma gwamnatin jihar Kano ta kafa wani kwamitin da zai rinƙa kula da ɗaukar ma’aikata bisa ƙa’ida a jihar.
A lokacin da yake ƙarin bayani yayin wani taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki ranar Laraba a Kano, shugaban kwamitin, Dakta Ibrahim Garba, ya ce za a miƙa daftarin dokar ga majalisar dokokin jihar da kuma gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, domin amincewa da dokar.
“Za’a ɗauki wannan mataki ne da nufin magance matsalar rashin aikin yi da kuma zaman kashe-wando tsakanin matasa a faɗin jihar Kano, “in ji shi”.
Kazalika, Garba ya bayyana cewa Gwamna Abba Yusuf, ya kafa kwamitin ne domin magance damuwar da ƴan jihar ke fuskanta dangane da yadda wasu kamfanoni masu zaman kansu suke ƙin ɗaukar ƴan asalin jihar aiki a kamfanonin su.

Manyan Labarai
Hisba za ta fara kamen matan auren masu zaman Majalisa a Kano

Hukumar Hisba ta jihar Kano ta ce za ta fara kamen matan auren da suke zaman majalisa a cikin unguwanni, domin daƙile matsalar da ake fuskanta tsakanin ma’aurata.
Mataimakin babban kwamandan hukumar Hisbah na jihar Kano Dakta Mujahideen Aminudden Abubakar, shi ke ya bayyana hakan a zanatawar sa da gidan rediyon Dala FM Kano, a ranar Laraba.
Ya ce hukumar ta lura da yadda zaman majalisar da wasu daga cikin matan aure suke yi, ke haifar da gulmace-gulmace, da yawo a gari, da kuma ɓatawa wasu rayuwa ta hanyar koya musu neman Mata da sauran Laifuka.
“Za mu sanya ƙafar Wando ɗaya da dukkanin matan aure masu zaman majalisa a cikin unguwanni, bisa yadda hakan ya saɓawa doka; jami’an mu za su fara yawo a cikin daren kaya don ɗakile wannan matsalar”in ji shi”.
Dr. Mujahedden, ya kuma yi kira ga magidanta da su ƙara kula da shige da ficen matan su, don gujewa fuskantar matsala a zamantakewar auren su.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi6 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su