Manyan Labarai
Delegates 17 sun dawo mun da kudi na bayan sun ki zaba ta – Sanata Ibrahim

Dan majalisa mai wakiltan yankin Kwara ta tsakiya, Sanata Ibrahim Oloriegbe, ya ce, wasu wakilai wato Deligate da ya baiwa kudade a lokacin zaben fidda gwani na jam’iyyar sun mayar masa da kudaden sa.
Sanatan ya bayyana haka ne a lokacin da ya fito a gidan talabijin na Channels Television na shirin Sunrise Daily, inda ya yi magana kan rikicin da ke tsakanin jam’iyyar mai mulki.
Sanata Oloriegbe ya caccaki tsarin da aka gudanar da zabukan fidda gwanin da aka fi yi a jihohin da aka fi zargin gwamnonin da dora wakilai a kan magoya bayan jam’iyyar.
“Babu wani majalisa; kamar a jiha ta, gwamna kawai ya zabo su (delegates) da daddare ya ce, mun yi primaries sai jerin suka zo. Don haka, ba ku ma san su waye wakilan ba… kuma hakan ya faru a jihohi da yawa, ”in ji shi.
“Ko a inda ake zabar mutane, ya kamata a ba su ‘yancin yin amfani da ikonsu ta hanyar zaben wanda suke so, amma abin ba haka yake ba. Gwamnonin sun zabo wadanda za su ba su umarni kuma wasu daga cikinsu sun yi rantsuwar kada kuri’a a inda gwamnonin ke jagorantar su…haka kuma ya faru a jihar Kwara.
“A zabe na (na firamare), wakilai 17 ne suka dawo don ba ni kudi na da na ba su na kayan aiki; wasu kuma ba don sun ce ‘muna so mu zabe ku ba, amma ba a ba mu damar kada kuri’a ba. Akwai wani abokin aikina a Kogi wanda ya ambata cewa mutane sun dawo (don mayar da kudinsa).”
Dan majalisar na cikin wasu ‘yan jam’iyyar da dama a majalisar dattawa da suka rasa tikitin jam’iyyarsu na neman sake tsayawa takara a cikin majalisar dokoki.
Yayin da wasun su suka fice daga jam’iyyar APC, wasu kuma wadanda ba su ji dadin ci gaban da aka samu ba, sun gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari domin neman sa baki.

Labarai
Za mu ci gaba da karɓar tsofaffin kuɗi a Singa har nan da kwanaki 2 – Habibu Fantiya

Wani ɗan kasuwa dake kasuwar Singa a jihar Kano ya ce, Alhaji Habibu Yusuf Abdullahi Fantiyahar zuwa nan da kwanaki biyu za su ci gaba da karbar kudade a shagunansu, sai dai idan bankuna sun yi musu barazanar daina karbar tsofaffin kudi za su dakata.
Alhaji Habibu Yusuf Abdullahi Fantiya, ya bayyana hakan ne a zantawarsa da wakilin mu na ‘yan Zazu, Abubakar Sabo, yana mai cewar, al’umma daga garuruwa daban-daban sun shigo kasuwar, idan suka daina karɓar tsofaffin kuɗi za a cutar da su.
Akwai cikakken rahoton a muryar da ke kasa.

Manyan Labarai
Majalisar dattijai ta bukaci CBN ya Kara wa’adin amfani da tsaffin kudi

Mako guda gabanin daina amfanin da tsaffin takardun kudaden naira 200 da 500 da Kuma 1000, majalisar dattawan Kasar nan ta bukaci Babban bankin kasa CBN da ya Kara wa’adin har zuwa 30 ga watan Yuni.
Cikin wani kudiri da sanata Sadik Suleman daga Jihar kwara ya gabatar a zaman majalisar na wannan rana.
Majalisar ta bukaci CBN da ya tsawaita lokacin har zuwa watanni 6 masu zuwa.
Majalisar ta kafa hujja da yanayin tattalin arzikin kasa, da Kuma korafe korafen jama’a, a don haka ta bukaci CBN da ya tsawaita lokacin amfanin da tsaffin kudin har zuwa 30 ga watan Yuni.
Batun sauyin takardun kudin dai na cigaba da samun mabanbantan ra’ayoyi daga ‘yan Nigeria, koda dai a baya bayan cikin wata tattaunawa da akayi da shugaban kasa Muhammadu Buhari, yace ” batun sauyin takardun kudin ba gudu ba ja da baya.

Manyan Labarai
Na sauke nauyin da ‘yan Nigeria suka dora min – Buhari

Shugaba Muhammadu Buhari ya ce ya mulki Najeriya da iyakar ƙokarinsa, inda ya ce bai ba wa ‘yan ƙasar kunya ba.
Shugaban wanda ya je jihar Bauchi a cigaba da ƴaƙin neman zaɓen jam’iyyar APC na shugaban ƙasa da kuma na gwamna, ya bayyana hakane lokacin da ya kai ziyara gidan Sarkin Bauchi, Dakta Rilwanu Suleiman Adamu.
Buhari ya ce dubban mutane da suke fitowa su tarbe shi a duk inda ya je hakan na nuna ƙarara irin soyayyar da ake masa.
“Ina so na faɗa cewa tsakanin 2003 zuwa 2011, na kai ziyara dukkanin ƙananan hukumomin Najeriya, sannan a 2019, lokacin da nake neman sake komawa kan mulki ƙaro na biyu, na ziyarci dukkanin jihohi a faɗin ƙasar, mutanen da naga sun fito tarba ta, abu ne da ba zan iya misaltawa ba saboda dandazonsu, a lokacin na yi alkawarin mulkar Najeriya da ‘yan Najeriya da iyaƙar ƙokarina kuma zuwa yanzu na san na yi ƙokari,” in ji shugaban.
Tun da farko a jawabinsa, Sarkin Bauchi, Dakta Rilwanu Suleiman, ya ce abu mai kyau ne idan shugabannin siyasa suka nuna girmamawa ga Sarakuna da kuma masarautu ta hanyar kai musu ziyara.
Ya godewa shugaba Buhari kan irin ci gaban da gwamnatinsa ta kawo a Bauchi, inda ya ce aikin haƙo man fetur na Kolmani, wani bu ne da ‘yan jihar da ma arewa maso gabas ba za su manta ba.

-
Nishadi3 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Manyan Labarai3 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai3 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Nishadi3 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai2 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Lafiya8 months ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Nishadi3 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su
-
Manyan Labarai3 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano