Connect with us

Ƙasashen Ƙetare

Masu zanga-zanga sun tirsasa shugaban kasa ya sauka daga mukaminsa a Sri Lanka

Published

on

Kakakin majalisar dokokin kasar Sri Lanka, Yapa Abeywardena, ya tabbatar da cewa, shugaban kasar, Gotabaya Rajapaksa, ya yi murabus daga mukamin sa.

Murabus din Mista Rajapaksa zai fara aiki ne daga ranar Laraba mai zuwa, domin ba da damar samun sauyi cikin sauki.

Ya ce, “Ya bukace ni da in sanar da kasar cewa, zai yi murabus a ranar Laraba 13 ga wata, saboda akwai bukatar mika mulki cikin lumana.

“Saboda haka babu bukatar sake tayar da hankali a kasar, kuma ina kira ga kowa da kowa ,saboda kasar da ya wanzar da zaman lafiya, domin samun damar mika mulki cikin kwanciyar hankali,” in ji kakakin a wata sanarwa da aka watsa ta gidan talabijin.

Mista Abeywardena ya bayyana hakan ne bayan da wasu fusatattun masu zanga-zangar suka kai wa gidan Mista Rajapaksa da na dan uwansa tsohon firaminista Mahinda Rajapaksa hari.

Murabus din shugaban ya fi kawo karshen daular Rajapaksa, wand Ya mulki kasar sama da shekaru goma, fiye da kawo karshen matsalar jin kai da kasar ke fuskanta.

Kasar ta fada cikin rikicin da ba a iya shawo kanta ba bayan karancin man fetur, da iskar gas da kuma kayan abinci da aka fara shafe watanni ana zanga-zangar da a yanzu ta kai ga korar shugabannin siyasarta.

Ƙasashen Ƙetare

Sojoji Sun yi juyin Mulki a Gabon

Published

on

Sojoji sun bayyana a gidan talabijin na kasar Gabon tare da sanar da karbi mulki.

Sun ce sun soke sakamakon zaben da ka gudanar ranar Asabar, inda aka ayyana shugaba Ali Bongo a matsayin wanda ya lashe zaben.

Hukumar zaben ta ce Mr Bongo ya samu nasara ne da kasa da kashi biyu bisa uku na kuri’un da aka kada a zaben da ‘yan adawa suka ce an tafka magudi.

Sun Kuma ce Hambarar da shi zai kawo karshen mulkin shekaru 53 da iyalan gidansu ke yi a Gabon.

Sojoji 12 ne suka bayyana a gidan talabijin dake sanar da soke sakamakon zaben tare da rusa dukkan hukumomin kasar.

Daya daga cikin sojojin ya fada a tashar talabijin ta Gabon 24 cewa, “Mun yanke shawarar kare zaman lafiya ta hanyar kawo karshen mulkin da ake yi a yanzu.”

Mr Bongo ya hau karagar mulki lokacin da mahaifinsa Omar ya rasu a shekara ta 2009.

Continue Reading

Ƙasashen Ƙetare

Sojoji sunyi juyin Mulki a jamhuriyar Nijar

Published

on

Rahotanni daga jamhuriyar Nijar na cewa Sojojin Kasar sun yi juyin Mulki, tare da sanar da kawo karshen mulkin shugaba Muhammad Bazum.

Cikin sanarwar da suka bayar a gidan telebijin din Kasar, jagoran tawagar sojojin Kanal Amadu Abdramane yace “mun kawo karshen mulkin shugaba Muhammad Bazum tare da karbe dukkanin Wani Iko”.

Sojojin dai sun bayar da dalilin halin rashin tabbas da Kuma Matsin tattalin arziki a kasar.

Tuni dai sojojin suka garkame dukkanin iyakokin Kasar tare da Sanya dokar takaita zirga zirga daga karfe 10 na dare zuwa 6 na safe.

Tun a safiyar laraba ne dai aka wayi gari da fara wancan yunkuri, Wanda yanzu haka ta tabbata, Kasar Nijar na hannun sojoji, Wanda shi ne Karo na hudu ana gudanar da juyin mulkin a jamhuriyar Nijar.

Continue Reading

Ƙasashen Ƙetare

An tsaurara tsaro a fadar shugaban Kasar Nijar

Published

on

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar, na nuni da cewa dakarun da ke gadin fadar shugaban ƙasa sun rufe duk wata hanyar shiga fadar a wani lamari da ba a kai ga ganowa ba.

Sai dai rahotanni na cewa yanzu haka wasu daga cikin tsofaffin shugabannin ƙasar ta Nijar na tattaunawa da sojojin domin sasanta lamarin.

Karin bayani nan tafe….

Continue Reading

Trending